Hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, ta ce, za ta rufe karbar kudin aikin hajjin 2022 daga masu niyyar zuwa aikin hajji a ranar 12 ga watan Mayu.
Ya ce, za a kawo karshen karɓar kuɗaɗen ne, saboda ayyukan hajjin na kara kusantowa.
Sakataren zartarwa na hukumar, Alhaji Mohammad Abba-Danbatta, ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai kan shirye-shiryen aikin hajjin 2022 a ranar Alhamis a Kano.
Abba-Danbatta ya bukaci dukkan maniyyatan da su kammala biyan kudin aikin hajjin su cikin kwanaki bakwai.
“Hukumar aikin Hajji ta kasa (NAHCON) ta kuma bayar da Naira miliyan 2 da digo 5 a matsayin wa’adin tafiyar da aikin na shekarar 2022 sakamakon tashin farashin dala da kuma karin kudaden haraji daga Saudiyya da kamfanin jiragen sama.
“Hukumar tana da akalla mutane 2,500 da suka bayar da wani kaso na kudaden aikin Hajji kuma za su ba da fifiko ga wadanda suka fara saka kudadensu ga hukumar,” inji shi.
Ya shawarci mutanen da suka haura shekaru 65 da su daina yunkurin sauya shekarsu, saboda hukumomin Saudiyya ba za su bari su shiga kasa mai tsarki ba.