Hukumar da ke kula da babban birnin tarayya Abuja ta rufe ma’aikatar ayyuka ta tarayya da hukumar kula da dabi’u ta tarayya da Merit house Maitama da Murg plaza kan basussukan sarrafa shara da ake bin hukumar kare muhalli ta Abuja (AEPB).
Da yake jawabi ga manema labarai yayin atisayen, Daraktan hukumar, Engr Osilama Briamah, ya ce, hukumomin da abin ya shafa sun ki biyan kudaden ayyukan hukumar.
Ya bayyana cewa, hukumar tana da makudan kudade da ta ke bi bashi ba tare da an mayar da martani daga wadanda suka gaza biya ba.
“Mun yi ƙoƙarin yin shawarwari don samun ingantacciyar hanya don cimma sakamako, amma babu wani amsa mai kyau; mun ba su tsarin biyansu amma da yawa daga cikinsu sun ki daukar damar da muhimmanci, sai hukumar ta bi hanyar da doka ta bi don kwato basussukan. Hukumar ta samu umarnin kotu na rufe harabar,” inji shi.