fidelitybank

Hujjoji na da ya sanya ni koma wa APC – Kawu Sumaila

Date:

Bayan jan ƙafa na tsawon lokaci, ɗaya daga cikin ƴan majalisar dattawa na jam’iyyar NNPP Sanata Abdurahman Kawu Sumaila ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Matakin na zuwa ne bayan shafe watanni ana takun saƙa tsakanin Sanatan da jam’iyyarsa ta NNPP a jihar Kano.

A makon da ya gabata ne Sanata Kawu Sumaila ya jagoranci wata tawagar yanmajalisar tarayya na NNPP inda suka gana da shugaban jam’iyyar APC mai mulki kuma tsohon gwamnan jihar Kano.

A hirar da ya yi da BBC, Sanatan ya bayyana dalilansa na ficewa daga jam’iyyar NNPP, inda ya tabbatar da cewa ya ɗauki matakin ne domin samar da ci gaba ga al’ummar mazaɓarsa.

Ya ce ”Wasu daga cikin dalilan da za su sa mu fice shi ne yankin da muka fito. Ya za mu iya samar wa mutanen yankin mu wani abu da zai amfanar da su, kuma ai ita siyasa da ƙunshi tattaunawa domin nema wa al’umma maslaha.”

Sanatan ya kuma yi watsi da batun cewa ya yi wa jam’iyyar NNPP butulci ganin cewa a ƙaƙashin inuwarta aka zaɓe shi inda ya yi nuni da cewa akasarin ƴan siyasa 109 da suka tsaya zaɓen majalisar dattawa a jam’iyyar ba su kai labari ba.

”Ai ba wai NNPP ɗin ba ce, waye ya tsaya a cikin NNPP ɗin,saboda haka ai zaɓa ta da aka yi kowa ya san an zaɓe ni ne saboda ni ne ɗantakaran, kuma a zone ɗin ai da sun tsaya, me ya sa ba su ci ba, sai yanzu? Saboda haka suna yana da tasiri.” in ji shi

Sanatan ya ƙara da cewa barinsa jam’iyya ba ta na nufin an ja zare tsakaninsa da gwamnatin NNPP a jihar Kano ba ne, inda ya ce a shirye ya ke ya goyi bayan duk wani shirin da gwamnatin za ta ɓullo da shi wanda zai kawo ci gaba ga al’umma.

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp