fidelitybank

Hujjoji na da ya sanya ni koma wa APC – Kawu Sumaila

Date:

Bayan jan ƙafa na tsawon lokaci, ɗaya daga cikin ƴan majalisar dattawa na jam’iyyar NNPP Sanata Abdurahman Kawu Sumaila ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Matakin na zuwa ne bayan shafe watanni ana takun saƙa tsakanin Sanatan da jam’iyyarsa ta NNPP a jihar Kano.

A makon da ya gabata ne Sanata Kawu Sumaila ya jagoranci wata tawagar yanmajalisar tarayya na NNPP inda suka gana da shugaban jam’iyyar APC mai mulki kuma tsohon gwamnan jihar Kano.

A hirar da ya yi da BBC, Sanatan ya bayyana dalilansa na ficewa daga jam’iyyar NNPP, inda ya tabbatar da cewa ya ɗauki matakin ne domin samar da ci gaba ga al’ummar mazaɓarsa.

Ya ce ”Wasu daga cikin dalilan da za su sa mu fice shi ne yankin da muka fito. Ya za mu iya samar wa mutanen yankin mu wani abu da zai amfanar da su, kuma ai ita siyasa da ƙunshi tattaunawa domin nema wa al’umma maslaha.”

Sanatan ya kuma yi watsi da batun cewa ya yi wa jam’iyyar NNPP butulci ganin cewa a ƙaƙashin inuwarta aka zaɓe shi inda ya yi nuni da cewa akasarin ƴan siyasa 109 da suka tsaya zaɓen majalisar dattawa a jam’iyyar ba su kai labari ba.

”Ai ba wai NNPP ɗin ba ce, waye ya tsaya a cikin NNPP ɗin,saboda haka ai zaɓa ta da aka yi kowa ya san an zaɓe ni ne saboda ni ne ɗantakaran, kuma a zone ɗin ai da sun tsaya, me ya sa ba su ci ba, sai yanzu? Saboda haka suna yana da tasiri.” in ji shi

Sanatan ya ƙara da cewa barinsa jam’iyya ba ta na nufin an ja zare tsakaninsa da gwamnatin NNPP a jihar Kano ba ne, inda ya ce a shirye ya ke ya goyi bayan duk wani shirin da gwamnatin za ta ɓullo da shi wanda zai kawo ci gaba ga al’umma.

legit latest news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp