fidelitybank

Hujjoji na da ya sanya ni koma wa APC – Kawu Sumaila

Date:

Bayan jan ƙafa na tsawon lokaci, ɗaya daga cikin ƴan majalisar dattawa na jam’iyyar NNPP Sanata Abdurahman Kawu Sumaila ya sauya sheƙa zuwa jam’iyyar APC.

Matakin na zuwa ne bayan shafe watanni ana takun saƙa tsakanin Sanatan da jam’iyyarsa ta NNPP a jihar Kano.

A makon da ya gabata ne Sanata Kawu Sumaila ya jagoranci wata tawagar yanmajalisar tarayya na NNPP inda suka gana da shugaban jam’iyyar APC mai mulki kuma tsohon gwamnan jihar Kano.

A hirar da ya yi da BBC, Sanatan ya bayyana dalilansa na ficewa daga jam’iyyar NNPP, inda ya tabbatar da cewa ya ɗauki matakin ne domin samar da ci gaba ga al’ummar mazaɓarsa.

Ya ce ”Wasu daga cikin dalilan da za su sa mu fice shi ne yankin da muka fito. Ya za mu iya samar wa mutanen yankin mu wani abu da zai amfanar da su, kuma ai ita siyasa da ƙunshi tattaunawa domin nema wa al’umma maslaha.”

Sanatan ya kuma yi watsi da batun cewa ya yi wa jam’iyyar NNPP butulci ganin cewa a ƙaƙashin inuwarta aka zaɓe shi inda ya yi nuni da cewa akasarin ƴan siyasa 109 da suka tsaya zaɓen majalisar dattawa a jam’iyyar ba su kai labari ba.

”Ai ba wai NNPP ɗin ba ce, waye ya tsaya a cikin NNPP ɗin,saboda haka ai zaɓa ta da aka yi kowa ya san an zaɓe ni ne saboda ni ne ɗantakaran, kuma a zone ɗin ai da sun tsaya, me ya sa ba su ci ba, sai yanzu? Saboda haka suna yana da tasiri.” in ji shi

Sanatan ya ƙara da cewa barinsa jam’iyya ba ta na nufin an ja zare tsakaninsa da gwamnatin NNPP a jihar Kano ba ne, inda ya ce a shirye ya ke ya goyi bayan duk wani shirin da gwamnatin za ta ɓullo da shi wanda zai kawo ci gaba ga al’umma.

nnnhausa

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haɗaka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...

An sake mayar da yan Najeriya 294 gida daga Nijar

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta Najeriya Nema ta...

An gano motoci 35 da aka sace a wata shida

Hukumar kiyaye haɗurra ta ƙasa a Najeriya ta ce...

Shugaban Laberiya ya je ta’aziyyar Buhari a Monrovia

Shugaban Ƙsaar Laberiya Joseph Nyuma Boakai ya kai ziyarar...

Rundunar Yansandan Kaduna ta hana gangamin goyon bayan Peter Obi

Rundunar 'yansandan Najeriya reshen jihar Kaduna ta hana gudanar...
X whatsapp