fidelitybank

Houthi sun harbo jirgin ruwan Amurka

Date:

Mayaƙan Houthi na Yemen sun yi iƙirarin kai hari kan wani jirgin ruwan Amurka a tekun Bahar Maliya, a wani sabon hari da suka kai kan jiragen jigilar kayayyaki.

Mayaƙan sun kira sunan jirgin da suka kai wa hari da KOI, wanda suka ce Amurka ke sarrafa shi.

Jami’an tsaron tekun sun ce wani jirgi da ke aiki a Kudancin tekun ya bayar da rahoton fashewar wani abu a yankin sai dai babu tabbacin ko jirgin da suke magana a kai ne.

A wani labarin, Amurka ta kai sabbin hare-hare kan jirage marasa matuƙa goma a Yammacin Yemen, wadanda ta ce mayaƙan na shirin kaddamar da hare-hare da su.

A cewar kamfanin dillancin labarai na Reuters, KOI wani jirgin dakon kayayyaki ne da kamfanin Birtaniya Oceonix ke tafiyar da shi.

Kakakin mayakan Houthi, Yahya Sarea ya ce jirgin ya nufi tashar jirgin ruwan yankin Falasdinawa da aka mamaye.

thisday news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...

An binne marigayi Muhammadu Buhari a gidansa na Daura

An binne gawar tsohon shugaban Najeriya Muhammadu Buhari a...

Pillars ta dauki yan wasa guda biyu

Kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars ta tabbatar da...

An cafke ‘yan Daba 28 a Kano

Rundunar ‘yan sandan jihar Kano ta ce ta samu...
X whatsapp