Tawagar matan Netherlands ta samu nasarar tsallakawa zuwa wasan dab da kusa da ƙarshe a gasar Kofin Duniya ta Mata, bayan da ta doke Afirka ta Kudu da ci 2-0.
Matan na Netherlands su ne suka zo na biyu a wasan cikin rukuni a gaban Amurka wadda ke riƙe da kofin.
A yanzu tawagar ta matan Netherlands za ta kara da Sifaniya wadda ta doke Switzerland 5-1 a ranar Asabar.