Hukumar Hisbah ta kama wasu mutane 11 a ranar Talata waÉ—anda aka ga suna cin abinci a lokacin azumin watan Ramadan a jihar Kano.
Jihar Kano – da ke da mafi rinjayen musulmi – ta kasance mai aiki da dokokin shari’a da tsarin addinin musulunci.
Hukumar ta hisbah kan gudanar da bincike a wuraren cin abinci da kasuwanni duk shekara a cikin watan Ramadan.
Kakakin hukumar, Lawal Fagge ya shaida wa BBC cewa an kama mutum 11, maza 10 da na mace É—aya da ba sa azumi.
“Mun kama mutane 11 a ranar Talata ciki har da wata mata da ke sayar da gyaÉ—a da aka ga tana cin kayanta inda wasu kuma suka sanar da mu,” .
“Sauran mutum 10 maza ne, kuma an kama su a fadin birnin musamman kusa da kasuwannin da ake tafka ta’asa.
Amma ya ce daga bisani an sake waÉ—anda aka kama bayan sun yi rantsuwar cewa ba za su sake shan azumi da gangan ba.
Ya kara da cewa za a ci gaba da gudanar da bincike amma ya ce an keɓe waɗanda ba musulmai ba.
“Ba mu kama waÉ—anda ba musulmai ba saboda wannan bai shafe su ba kuma kawai lokacin da za su iya yin laifi shi ne idan muka gano suna dafa abinci don sayar wa musulmi da ya kamata yana azumi.”
Kimanin shekaru 20 da suka gabata ne aka ɓullo da shari’ar Musulunci domin ta dace da dokokin da ba ruwansu da addini a jihohi 12 na arewacin Najeriya, waɗanda galibinsu Musulmi ne.
Watan Ramadan na da matukar muhimmanci a Musulunci.