fidelitybank

Hisbah ta fara kwashe yaran da ke gararamba a kan titunan Kano

Date:

Gwamnatin Kano ta fara kwashe ‘dubban’ yara da ke rayuwa a kasuwanni da ƙasan gadoji a Kano, babban birnin jihar.

Gwamnatin ta fara ɗaukar matakin ne a jiya Litinin, inda ta samar da wani sansanin ajiyewa da kuma tantance yaran.

Shugaban hukumar Hisbah a jihar, Sheikh Aminu Daurawa ya ce “mun samu rahoton akwai ɗaruruwa ko kuma dubban ƙananan yara da ba su haura shekara 15 ba waɗanda suke kwana a ƙarƙashin gadoji da cikin tashoshi da kuma kasuwanni.”

“Ci gaba da rayuwarsa a waɗannan wurare zai iya haifar da matsala ta tsaro da ta zamantakewa a nan gaba,” in ji Daurawa.

Shugaban na hukumar Hizba ya ce alƙaluman da suke da su sun nuna cewa akwai irin waɗannan yara masu gararamba a kan tituna sama da 5000.

Ya kuma bayyana cewa za a tara yaran da aka kwashe ne a wata cibiya, inda za a tantance su, sannan a san matakan da za a ɗauka.

Kano ce jiha mafi yawan al’umma a arewacin Najeriya, kuma ɗaya daga cikin waɗanda ke da yawan ƙananan yara waɗanda ba su zuwa makaranta.

Duk da cewa jihar na daga cikin waɗanda suka sanya hannu kan dokar kare hakkin yara a Najeriya, amma har yanzu akwai dubban yara da ke tallace-tallace ba tare da zuwa makaranta ba, yayin da wasu yaran kuma ke barace-barace a kan tituna da sunan neman ilimin addini.

Sheikh Daurawa ya ce bayan kammala tantance yaran, da inda suka fito, za a sanya wasu daga cikinsu makaranta yayin da za a koya wa wasu sana’a.

Ya kuma bayyana cewa akwai yiwuwar gurfanar da wasu iyayen da aka tsinci yaran nasu na gararamba kan titi, a gaban kotu.

“Wanda ya yi sakaci ya bar ɗansa yana yawo a kan titi duk da cewa yana da halin ɗaukar nauyinsa, to za mu gurfanar da shi a gaban kotu”.

Sai dai ya ce yaran da ba su da iyaye ko waɗanda rikici ya tarwatsa – gwamnatin za ta ɗauki matakin gyara musu rayuwa ta hanyar ba su ilimi da koya musu sana’a.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp