Hukumar Hisbah ta jihar Jigawa ta kama wasu tarin mata 44 da suka hada da maza 17 a karamar hukumar Taura bisa zargin aikata badala.
Kwamandan hukumar Hisbah, Malam Ibrahim Dahiru, a jihar ne ya bayyana haka ga kamfanin dillancin labarai na kasa (NAN) a Dutse ranar Talata.
Ya kara da cewa, jami’an ‘yan sanda tare da hadin gwiwar ‘yan sanda sun kama wadanda ake zargin ne a ranar Litinin a babban garin ‘Gujungu’.
A na zargin matan 44, masu aikata jima’i a kasuwanci. Mutanen 17, an kama su ne a lokacin da ‘yan sandan suka kai farmaki yankin da misalin karfe 6 na safe.