fidelitybank

Hisba ta kori wasu ma’aikatan ta a Kano

Date:

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kori daya daga cikin kwamandojin ta saboda hada da yin zagon kasa ga yaki da lalata da zamantakewa a jihar.

Babban kwamandan Hisbah, Sheikh Aminu Daurawa, ya tabbatar wa manema labarai hakan a ranar Talata a Kano, inda ya ce wasu jami’an guda biyar kuma suna kan bincike.

A cewarsa, “Ma’aikatan da aka kora galibi suna hada baki ne da miyagun abubuwa domin su tafka munanan ayyuka a jihar.”

Daurawa ya kara da cewa ya kuma kori mataimakin Sufeto na Hisbah (DSH) tare da bayyana cewa ana neman sa, inda ya ce duk inda aka same shi a kama shi a gurfanar da shi a gaban kuliya.

Ya ce mataimakin Sufetan da aka kora ya saba hada kai da ma’aikatan otal din don kada hukumar Hisbah ta kai farmaki a yayin gudanar da ayyukanta.

Ya kuma yi watsi da rade-radin da wani ma’abocin Facebook ke yi na cewa jami’an sa sun yi wa wasu aski wanda ba dan asalin jihar ba da kwalba bayan sun kai farmaki gidan karuwai a jihar.

Ya kuma bayyana zargin a matsayin na ā€˜yan ta’adda ne, inda ya ce hukumar Hisbah ta gano wanda ya wallafa faifan bidiyon, kuma za a gayyaci wanda ake zargin domin ya tabbatar da ikirarinsa.

national news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar Ę“ansandan jihar Kaduna, sun buʙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ʙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ā€˜Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ʙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ā€˜yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp