fidelitybank

Hisba ta kama mota ɗauke da kwalaben giya 8,600 a Kano

Date:

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama kwalaben barasa 8,600 a cikin wata mota da ta zo jihar daga Kaduna.

Jami’in hukumar mai kula da kayan maye, Idris Ibrahim, wanda ya bayyana hakan ga manema labarai a karshen mako, ya ce an kama barasa a ranar Alhamis din da ta gabata a kauyen Kwanar Dangora, da ke kan hanyar Kano zuwa Kaduna.

A cewarsa, jami’an hukumar sun yi ta bin diddigin motar daga Kaduna har ta shigo cikin yankin Kano.

“Mun tsayar da motar a kauyen Kwanar Dangora kuma direban ya yi yunkurin tserewa amma jami’an mu sun kama shi.

by TaboolaSponsored Links Kuna Iya So
Har zuwa Bonus 200,000!
Betano
“Kun san haram ne sayar da giya a jihar Kano. Don haka za mu gurfanar da direban a gaban kuliya bayan mun kai maganarsa,” inji shi.

Ibrahim ya ci gaba da cewa, tawagar Hisbah da ke kula da ayyukan sa maye a hukumar tana jiran karin umarni daga hukumar Hisbah.

Kazalika ta kama wasu mata 15 da laifin karuwanci yayin gudanar da ayyuka a sassa daban daban na cikin birnin Kano.

An kama matan da ake zargi da aikata karuwanci a Hotoro Tishama, Kogin Bakin Verd Sabon Gari, titin Miyangu, titin Hadejia da kuma tsoffin wuraren ajiye motoci na Zoo Road.

Mataimakin babban kwamandan hukumar, Dakta Mujahid Aminuddeen, wanda ya tabbatar da kamen, ya ce an kama wasu daga cikin wadanda ake zargin karuwai sau da yawa, kuma an gurfanar da su a gaban kotu, amma har yanzu suna gudanar da wannan sana’ar ta haramtacciyar hanya.

“Abin takaici ne yadda wasu daga cikin wadannan matan suka bar jihohinsu da kasashensu suka zo Kano inda suke yin karuwanci da wasu munanan dabi’u.

“Suna yawo a kan titunan Kano suna yin abubuwa iri-iri. Muna kira ga jama’a da su ci gaba da kai rahoton irin wadannan ayyuka domin mu tsaftace jihar,” ya kara da cewa.

latest news nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp