Hukumar Hisba a Kano, ta fara shirin kama matan da su ke talla a kan titunan jihar.
Kafar yada labaran Radio Najeriya ta rawaito, mataimakiyar mukaddashin kwamanda mai kula da harkokin mata, Malama Ummulkulsum Kasim ce, ta yi wannan bayanin, bayan kama wasu mata a titunan karamar hukumar Kumbotso.
Malama Ummulkulsum ta ce, yawancin matan da ke talla akan tituna da daddare ‘yan mata ne da ke saida gyara da goro, da rogo, ko kayan lambu da sauransu.
Ta ce, yawancin ‘yan tallan an gano su a tashoshin mota, da wurin makanikai abin takaicin kuma da daddare.
Malama Ummulkulsum ta ce, ”hakkin iyaye ne killace ‘ya’yansu da tabbar da ba su tarbiyya da ilimi, da kare su daga aikata ba daidai ba. Kuma addinin musulunci ya tabbatar da hakan, bai kamata a bar ‘ya’ya mata da na yawo kara zube da sunan talla ba.”
Radio Nigeria ta rawaito kwanakin da suka gabata hukumar Hisba a jihar Kanon ta yi nasarar kama wasu matasa 19 kan zargin halartar auren jinsi a Kano, ko da ya ke Amarya da Angon sun tsere har yanzu ba a san inda suka buya ba.