Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta kama wasu mutane 10 da suka hada da mata takwas da maza biyu, bisa zarginsu da yawon ddare a sassa daban-daban na jihar.
An yi kamen ne a wani bangare na yakin da ake yi na “Operation Clean Up” da nufin inganta zaman lafiyar jama’a da kuma kula da tsaftar kawar da baɗala.
Da yake zantawa da manema labarai, mukaddashin kwamandan Hisbah, Aminudden Mujahiddeen, ya bayyana cewa an kama mutanen ne a tashar mota ta Kofar Ruwa, titin filin jirgin sama, Sabon Gari, da sauran wurare.
Ya bayyana cewa wasu daga cikin wadanda aka kama ana zarginsu da safarar miyagun kwayoyi da kuma nemansu. “Wasu ma ba ’yan Kano ba ne. Hasali ma daya daga cikin matan ba ‘yar Najeriya ba ce,” Mujahiddeen ya bayyana.
Ya kuma tabbatar wa da jama’a cewa ana ci gaba da gudanar da bincike kuma za a dauki matakin da ya dace a wani bangare na kokarin tabbatar da doka da oda a jihar.