fidelitybank

Hisba na neman su Murja ruwa a jallo a Kano

Date:

Hukumar Hisbah ta jihar Kano ta tabbatar da sanarwar neman wasu shahararrun masu amfani da shafin Tiktok guda shida saboda furta kalaman batsa cikin wasu bidiyo da suka yi, lamarin da ya ci karo da dokar tabbatar da tarbiyya.

Shugaban hukumar Sheikh Aminu Ibrahim Daurawa ya shaida wa BBC cewa cikin masu amfani da shafin da ake nema akwai Abubakar Ibrahim da aka fi sani da Gfresh sai Sadiya Haruna da Ashiru Idris da aka fi sani da Maiwushirya da Ummee Shakira da Murja Ibrahim Kunya da kuma Hassan Makeup.

A cewar Sheikh Daurawa, suna cigiyar mutanen ne bayan É“ullar wani bidiyo da a ciki suke furta kalaman da ba su dace ba wanda kuma ya ci karo da alkawarin da suka yi lokacin da aka kama su a karon farko domin yi musu wa’azi.

Ya ce babban burin Hisbah shi ne ta ga an gyara kura-kurai tun da “ba so muke mu ci gaba da gayyato mutanen ba, watakila hakan zai sa su ji cewa ba su kyauta ba tun da an yi yarjejeniya da su, sun yi mana alkawari za su gyara [amma hakan ba ta faru ba].”

Sheikh Daurawa ya ce kasancewar wannan ne karo na biyu da suke saba dokar ta tarbiyya, ko da sun bayyana a gaban Hisbah, za su sake jan hankalinsu a kan yin irin wadannan dabi’u tare da tabbatar da cewa sun rubuta alkawarin riko da yarjejeniyar da aka yi da su.

Ya ce sai mutum ya taka doka sau uku sannan ake gurfanar da shi a gaban kotu.

“Ba kotu za mu kai su ba yanzu, ai yarjejeniya sau uku ake yi, idan suka zo, za mu ce musu ya muka yi yarjejeniya da ku, bayan kun gaya mana ba za ku sake ba kuma kuka sake, sai mu ji uzirinsu.” in ji Sheikh Daurawa.

Shugaban hukumar ta Hisbah ya ce a baya, sun tattauna da jami’ai daga ofishin Tiktok da ke Legas inda kuma suka ce idan aka samu masu amfani da Tiktok da yake saba doka ko jayo tashin hankali ko É“ata addini “idan muka rubuta muka kai musu, suka bayar da rahoto, za a iya toshe [shafinsa].”

“Wannan ma ya fi yi wa dan Tiktok zafi, ka sa a goge shafinsa domin wani ya tara mabiya da yawa, idan ya ji za a rufe shafinsa saboda gwamnati ta shigo, kuma doka ya karya.” in ji Daurawa.

A shekarar da ta gabata ne hukumar ta Hisbah ta gana da yan Tiktok a Kano domin tattaunawa da su game da yadda za a tabbatar da kyawawan dabi’u tare da kawar da fitsara a shafin.

today daily post news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...

Musulman Nijeriya a cigaba da jajircewa – Obi

Ɗan takarar shugaban ƙasa a karkarshin jam'iyyar Labour a...

Akwai takaici ambaliyar Neja – IBB

Tsohon shugaban ƙasa, Janar Ibrahim Babangida, ya kwatanta ambaliyar...

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar Æ´an Æ™asarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...
X whatsapp