Ƙungiyar Hezbollah ta ce ta harba gwamman makaman roka zuwa garin Safed da ke arewacin Isra’ila.
Sojojin ƙasar sun ce sun gano wasu rokoki kusan 50, waɗanda aka kakkaɓo wasu daga cikinsu.
Kawo yanzu dai babu rahoton asarar rayuka.
Hakan na zuwa ne a daidai lokacin da Isra’ilar ta kai wani hari kudancin birnin Beirut da sanyin safiyar yau Laraba.
Dama sojojin Isra’ilar sun ba da umarnin kwashe mazauna yankin nan take.