Jagoran addinin Iran Ayatollah Ali Khamenei ya ce, ‘Hezbollah ce ke da nasara’ kamar yadda ya wallafa a shafinsa na X a safiyar yau Laraba, wanda shi ne karo na farko da jagoran na addini ya fito ya yi magana a game da hare-haren Isra’ila a Lebanon.
Jawabin na Ayatollah Ali Khamenei na zuwa ne a daidai lokacin da ake ce-ce-ku-cen Iran na goyo wa Hezbollah baya da tallafin kuɗaɗe da kayan yaƙi.
A jawabinsa a New York a ranar Litinin, shi ma Shugaban Iran Masoud Pezeshkian ya ce ba sa fatan ta’azzarar yaÆ™i a Gabas ta Tsakiya, inda ya Æ™ara da cewa ko yaÆ™in ya Æ™azanta, babu Æ™asar da za ta ci riba.
Shi ma shugaban kwamitin makamashin nukiiya na MDD, Rafael Grossi a zantawarsa da Reuters ya bayyana cewa ya ga alamar Iran ta shirya tattaunawa a game da shirinta na nukiliya, sannan ya ce zai ziyarci ƙasar a watan Oktoba.