Da safiyar ranar Asabar ne ƙungiyar Hezbollah a Lebanon ta ce ta harba makamai masu linzami zuwa ɓangaren da ‘cibiyar kula da sararin samaniyar Isra’ila take’, a wani abu da ta bayyana da ramuwar gayya kan kisan da aka yi wa mataimakin shugaban kungiyar Hamas a Beirut, Saleh Al-Arouri.
Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ce cikin wata sanarwa da Hezbolla ta fitar ta ce ”a wani martani na kisan Sheikh Saleh Al-Arouri da wasu ‘yan uwansa a kudancin birnin Beirut, ƙungiyar ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami aƙalla 62 kan cibiyar kula da sararin samaninar Isra’ila ta Meron.
Sanarwar ta ƙara da cewa ƙungiyar ta samu tabbacin cewa makaman sun shafi cibiyar.
Cibiyar Meron – wadda ke kan tsaunin Jarmaq da ke arewacin ƙasar – na ɗaya daga cikin cibiyoyi biyu da Isra’ila ke amfani da su wajen lura tare da kare sararin samaniyarta.
AFP ya ce sojojin Isra’ila sun bayyana kakkaɓo hare-haren makamai masu linzami kimanin 40 da aka harbo daga ƙasar Lebanon a ranar Asabar da safe a ɓangaren cibiyar Meron.
An yi ta jin ƙarar na’urar ankararwa a biranen da ke arewacin Isra’ila da ɓangaren tuddan Gola.
A ranar Talatar da ta gabata ne wani hari da aka yi amanna na jirgi maras matuƙi ne a birnin Beirut ya yi sanadin kisan Saleh Al-Arouri.
Inda hukumomin Lebanon da ƙungiyar Hamas da Amurka suka zargi Isra’ila ta kai harin, to sai dai Isra’ila ba ta ɗauki alhakin harin ba.