fidelitybank

Hezbollah ta yi lugudan wuta a kan Isra’ila

Date:

Da safiyar ranar Asabar ne ƙungiyar Hezbollah a Lebanon ta ce ta harba makamai masu linzami zuwa ɓangaren da ‘cibiyar kula da sararin samaniyar Isra’ila take’, a wani abu da ta bayyana da ramuwar gayya kan kisan da aka yi wa mataimakin shugaban kungiyar Hamas a Beirut, Saleh Al-Arouri.

Kamfanin dillancin labarai na AFP ya ce cikin wata sanarwa da Hezbolla ta fitar ta ce ”a wani martani na kisan Sheikh Saleh Al-Arouri da wasu ‘yan uwansa a kudancin birnin Beirut, ƙungiyar ta kaddamar da hare-haren makamai masu linzami aƙalla 62 kan cibiyar kula da sararin samaninar Isra’ila ta Meron.

Sanarwar ta ƙara da cewa ƙungiyar ta samu tabbacin cewa makaman sun shafi cibiyar.

Cibiyar Meron – wadda ke kan tsaunin Jarmaq da ke arewacin ƙasar – na ɗaya daga cikin cibiyoyi biyu da Isra’ila ke amfani da su wajen lura tare da kare sararin samaniyarta.

AFP ya ce sojojin Isra’ila sun bayyana kakkaɓo hare-haren makamai masu linzami kimanin 40 da aka harbo daga ƙasar Lebanon a ranar Asabar da safe a ɓangaren cibiyar Meron.

An yi ta jin ƙarar na’urar ankararwa a biranen da ke arewacin Isra’ila da ɓangaren tuddan Gola.

A ranar Talatar da ta gabata ne wani hari da aka yi amanna na jirgi maras matuƙi ne a birnin Beirut ya yi sanadin kisan Saleh Al-Arouri.

Inda hukumomin Lebanon da ƙungiyar Hamas da Amurka suka zargi Isra’ila ta kai harin, to sai dai Isra’ila ba ta ɗauki alhakin harin ba.

vgn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Kare Ya Kashe Ragon Layya: Mai ƙwacen waya ya kashe Sojin ruwa a Kaduna

Wani mai ƙwacen waya ya kashe wani soja bayan...

Sojoji sun hallaka ƴan Boko Haram da dama

Da sanyin safiyar ranar Litinin, dakarun rundunar Haɗin kai...

Tarzomar kama baƙin haure a Amurka na yamutsa hazo

An shiga rana ta uku a tarzomar da ake...

Alhazai sun kammala aikin Hajji bana

A ranar Lahadin da ta gabata ne alhazai miliyan...

Tinubu gyaran ƙasa za ka mayar da kai ba zaɓen 2027 ba – ACF

Ƙungiyar Tuntuɓar Juna ta Arewacin Najeriya, ta yi kira...

Ƴan Jagaliya sun caka wa Matashi kuwa lokacin da ya zo karɓar naman Sallah a Kano

Matashi Ibrahim Mahmud ya rasu sakamakon caka masa wuƙa...

Kallo Ya Koma Sama: Elon Musk zai fuskanci mummunar sakamako – Trump

Ana ci gaba da takun saka tsakanin shugaban Amurka...

Zulum ya miƙa kyautar Naira miliyan 100 ga iyalan Sojojin da aka kashe

Gwamna Babagana Umara Zulum na jihar Borno, ya bai...

Otal ɗin ƴan Najeriya ya kama da wuta wani ɓangaren a Saudiyya

Hukumar Alhazai ta Najeriya ta ce an samu tashin...

An kai hari maɓoyar Boko Haram a Borno

Biyo bayan sahihan bayanan sirri da aka samu, rundunar...

Alaƙar Trump da Elon Musk ta yi tsami sosai

Attajirin da ya fi kowa arziki a duniya, Elon...

An yi jana’izar Muhammad Uwais

An gudanar da jana'izar tsohon alkalin alkalan Najeriya, mai...
X whatsapp