An ga hayaƙi na tashi a birnin Haifa da ke arewacin Isra’ila sakamakon jerin hare-haren rokoki daga Lebanon a daren ranar Lahadi.
Wasu magidanta da gidajensu suka kama da wuta sun samu raunuka. Tawagar masu aikin ceto sun isa wuraren da bain ya shafa domin duba lafiyar waɗanda suka ji raunukan, a daidai lokacin da dakarun Isra’ila suka killace yankunan.
Birnin na Haifa dai yana kudancin Isra’ila ne abin da ke nuni na cewa yanzu hare-haren Hezbollah sun fara isa kudanci maimakon takaice su a arewaci.