fidelitybank

Haɗin gwiwa ne zai baiwa PDP damar karɓar mulki a shekarar 2023 – Bukola Saraki

Date:

Tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, ya ce, matakin da wasu ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP suka dauka na kafa hadin gwiwa zai baiwa jam’iyyar damar karbar mulki daga hannun jam’iyyar APC a shekarar 2023.

Wata sanarwa a jiya, ta hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Bayelsa, Daniel Alabrah, ta ce, mai fatan zama shugaban kasar ya yi magana ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawar sirri da takwaransa Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto da kuma Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi, tare da Gwamna Douye Diri a Gidan Gwamnati na Creek Haven a Yenagoa, Jihar Bayelsa.

Saraki ya bayyana cewa: “Mun zo nan ne domin mu tuntubi gwamnan kan kokarin da muke yi na samun dan takarar da ya dace. Kamar yadda kuka sani, mu uku ne suka nuna sha’awar tsayawa takara a jam’iyyar PDP. Mun yi ta zagawa da shugabannin jam’iyyar mu. Gwamnan Bayelsa ba jagora ne kawai ba, har ma babban mai ruwa da tsaki, wanda ke da rawar da zai taka a zaben 2023.

“Kiranmu ga ‘yan Najeriya shi ne mu ji radadin ku, kunci da rashin tsaro. Shi ya sa burinmu shi ne mu mayar da kasar nan PDP mu kyautata rayuwarku. Mun zo ne don neman goyon bayan ku yayin da muke gabatowa 2023. Mun yi magana sosai kuma muna jin kwarin gwiwa daga kalaman gwamna. Yanzu bari mu fara gina wadannan tubalan da za su tabbatar da cewa PDP za ta inganta Najeriya.”

A nasa jawabin, Diri ya bukaci jam’iyyar PDP da ta samar da hadin kai idan jam’iyyar na son lashe zabe mai zuwa.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Talauci da rashin tsaro na iya barazana ga zaɓen 2027 – Rahoto

Ƙungiyar fafutikar kare haƙƙin ɗan'adam da tabbatar da dimokuraɗiyya...

Tinubu ya aike da sakon ta’aziyya ga iyalan Dantata

Shugaban kasa, Bola Tinubu ya aike da saƙon ta'aziyarsa...

Dangantaka tsakanin Amurka da Canada ta yi tsami

Shugaban Amurka Donald Trump ya ce zai yanke dukkan...

An yi jana’izar Kwamandojin sojinta da masana nukiliyar Iran da Isra’ila ta kashe

Iran ta gudanar da jana'izar mutum 60, ciki har...

Za a binne Attaijirin dan kasuwar nan na Kano Dantata a Dubai

Allah ya yi wa attajirin ɗan kasuwar nan na...

Dalori ne ya maye gurbin Gnaduje a shugabancin APC

Mataimakin shugaban jam'iyyar APC na yankin arewa, Ali Bukar...

IGP ya ba da umarnin bincike kan bidiyon ƙorafin wani tsohon ɗansanda

Babban Sufetan ‘Yan Sandan Najeriya, Kayode Adeolu Egbetokun, ya...

Amurka za ta bayar da gudunmawar dala miliyan 30 ga ‘yan Gaza

Amurka za ta ba da tallafin dala miliyan talatin...

Iran na binciken ɓarnar da aka yi cibiyoyin nukiliyar ƙasar

Ministan harkokin waje na Iran ya amince an yi...

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karo na farko

Japan ta zartar da hukuncin kisa a karon farko...

Sojoji na zaman makoki na kwanaki 3 bayan an kashe Jami’ai 17

Rundunar Sojin sama ta bayyana fara zaman makoki na...

‘Yan Ta’adda ba za su samu mafaka ba a Nasarawa ba – Gwamna

Gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule ya musanta zargin da...
X whatsapp