Tsohon shugaban majalisar dattawa, Dakta Bukola Saraki, ya ce, matakin da wasu ‘yan takarar shugaban kasa a jam’iyyar PDP suka dauka na kafa hadin gwiwa zai baiwa jam’iyyar damar karbar mulki daga hannun jam’iyyar APC a shekarar 2023.
Wata sanarwa a jiya, ta hannun babban sakataren yada labaran gwamnan jihar Bayelsa, Daniel Alabrah, ta ce, mai fatan zama shugaban kasar ya yi magana ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai bayan ganawar sirri da takwaransa Gwamna Aminu Tambuwal na jihar Sokoto da kuma Gwamna Bala Mohammed na Jihar Bauchi, tare da Gwamna Douye Diri a Gidan Gwamnati na Creek Haven a Yenagoa, Jihar Bayelsa.
Saraki ya bayyana cewa: “Mun zo nan ne domin mu tuntubi gwamnan kan kokarin da muke yi na samun dan takarar da ya dace. Kamar yadda kuka sani, mu uku ne suka nuna sha’awar tsayawa takara a jam’iyyar PDP. Mun yi ta zagawa da shugabannin jam’iyyar mu. Gwamnan Bayelsa ba jagora ne kawai ba, har ma babban mai ruwa da tsaki, wanda ke da rawar da zai taka a zaben 2023.
“Kiranmu ga ‘yan Najeriya shi ne mu ji radadin ku, kunci da rashin tsaro. Shi ya sa burinmu shi ne mu mayar da kasar nan PDP mu kyautata rayuwarku. Mun zo ne don neman goyon bayan ku yayin da muke gabatowa 2023. Mun yi magana sosai kuma muna jin kwarin gwiwa daga kalaman gwamna. Yanzu bari mu fara gina wadannan tubalan da za su tabbatar da cewa PDP za ta inganta Najeriya.”
A nasa jawabin, Diri ya bukaci jam’iyyar PDP da ta samar da hadin kai idan jam’iyyar na son lashe zabe mai zuwa.