Rahotanni na cewa Haɗaddiyar Daular Larabawa, (UAE) ta bai wa Najeriya taimakon abinci tan 50 domin tallafa wa waɗanda ambaliar ruwa ta ɗaiɗaita.
Mai magana da yawun hukumar agajin gaggawa ta NEMA, Manzo Ezekial a wata sanarwa da ya fitar ranar Litinin ya ce ambasadan UAE, Salem Alshami ya miƙa kayan tallafin ga hukumar.
Ambasadan ya shaida cewa tallafin ya samu ne sakamakon kuɗurin shugaban UAE, Sheikh Mohammed Al Nahyan na ganin ya tallafa wa waɗanda iftila’in ambaliyar ruwa ya faɗawa.
Manzo ya ce manyan jami’an hukumar NEMA da ma’aikatar ƙasashen waje da kuma ofishin mai bai wa shugaban ƙasa shawara kan harkokin tsaro.