fidelitybank

Hayagaga kawai a Atiku ya ke yi da zafin kayi – Tinubu

Date:

Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu, ya yi watsi da bayanan da abokin takararsa na babbar jam’iyyar hamayya ta PDP a zaben da ya gabata, Atiku Abubakar, ya yi, cewa ya tattara isasshiyar shaidar da za ta tabbatar wa kotu, cewa shugaban kasar ya gabatar da takardar shaidar karatun digiri ta bogi ga hukumar zabe.

Shugaban Najeriyar, ya ce bakin alkalami ya riga ya bushe, dangane da gabatar da wata hujja, idan ma akwai ta a shari’ar zaben shugaban kasa.

Cikin wata hira da BBC, mai magana da yawun shugaban kasar Abdul’Aziz Abdul’Aziz, ya ce abin da shi tsohon mataimakin shugaban kasa ya fada su a wajensu abu ne na su tausaya masa.

Ya ce, “ Wadannan bayanai na Atiku abu ne na a yi masa jaje saboda ya nuna cewa a cikin rudani yake bai ma san abubuwan da ke faruwa ba.”

Abdul’aziz Abdul’aziz, ya ce ita jami’ar da ake magana a kanta ta jihar Chicago da ke kasar Amurka a dukkannin takardu da bayanai da suka ba wa kotu babu inda suka ce akwai takardar bogi ko kuma shi Tinubu bai yi karatu a wajensu ba.

Ya ce, “ Bisa la’akari da wannan hujjar shi dan takarar jam’iyyar PDP Atiku Abubakar, ya yi maganganu ne wadanda yawancinsu na soki-burutsu ne da kuma kokarin yi wa mutane bayanan da za su dugunzuma su ko ma su kawo rashin fahimta.”

Mai magana da yawun Shugaba Tinubun, ya ce babu wata magana ta a zo a gani, borin kunya ne irin na wanda ya sha kaye.

“ Ko da mutumin da bai yi karatun lauya ba ya san cewa kotunan da suke na daukaka kara ba kotuna ba ne na yin shari’a, kotuna ne na duba hukuncin da kotun kasa ta yi domin idan akwai kuskure sai a gyara ko a canja wannan hukunci ko ma a tabbatar da shi.” In ji shi.

Abdul’aziz, ya ce, idan Atiku Abubakar na tunanin ya samo wata hujjar da yake gani zai iya gabatarwa ai bakin alkalami ya riga ya bushe.

Ya ce , “ Ba mu da wata fargaba saboda duk abin da ya kamata a yi an yi don abin da ake bukata wannan makaranta da ake ta magana a kanta ta riga ta bayar.”

“ Sannan mun san cewa duk abin da yake yi ba shi da tasiri kuma ba shi da wani gurbi na shari’a,” in ji shi.

Mai Magana da yawun shugaban na Najeriya, ya ce ya kamata yanzu Atiku Abubakar ya gane cewa an rufe babin siyasa kamata ya yi a fuskanci babin gina kasa kawai kamar yadda shi Shugaba Tinubu ya sha fada.

www nnn news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp