fidelitybank

Hauhawar farashi ya kai 24.48 cikin 100 a Najeriya – NBS

Date:

Hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta ce alƙaluman hauhawar farashi sun koma 24.48 cikin 100 a watan Janairun da ya gabata.

Wannan ne karon farko da National Bureau of Statistics (NBS) da fitar da rahoton bisa sabon tsarin tattara alƙaluma da ta fara amfani da shi, abin da ke nufin da wuya a iya a iya gane haƙiƙanin raguwa ko hauhawa a yanzu.

Alƙaluman sun nuna cewa hauhawar farashin kayan abinci ta kai 26.08 idan aka kwatanta da shekarar da ta gabata.

Kafofin yaɗa labarai na Najeriya sun ruwaito shugaan hukumar, Prince Adeyemi Adeniran, na faɗa ranar Talata cewa sun sauya tsarin ne saboda “daidaita shi da irin na sauran ƙasashen duniya”.

Ya ce karo na ƙarshe da Najeriya ta sauya tsarin ƙididdigar shi ne a shekarar 2009, inda ake ƙididdige farashin kayan da aka fi amfani da su a wannan tsakanin.

Hakan na nufin yanzu za a dinga kwatanta farashin kayayyakin da aka ƙididdige daga shekarar 2024, maimakon 2009 da aka dinga amfani da ita a baya.

“A sabon tsarin, ba matso da alƙaluman kusa da halin da ake ciki kawai muka yi ba, mun kuma ƙaddamar da sabuwar hanyar tattara bayanai don inganta yadda muke adana su da kuma sahihancinsu,” in ji shi.

www.nnn.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp