fidelitybank

Hauhawar farashi na shafar Najeriya – MDD

Date:

Wani rahoto da Majalisar Ɗinkin Duniya ta fitar, ya bayyana cewa hauhawar farashin kayan abinci da ƙaruwar farashin dala na shafar ‘yan Najeriya da wasu ƙasashe masu tasowa.

Rahoton ya ce waɗannan al’amura biyu sun tilasta wa mutane da dama a ƙasashe masu tasowa daina yin wasu muhimman abubuwa, ciki har da rashin samun abin da za su ci, da tilasta wasu cire ‘ya’yansu daga makarantu.

Rahoton wanda aka fitar cikin watan Disamba ya ce farashin abinci ya ƙaru a ko’ina, inda ya kai matakin da ba a taɓa ganin irinsa ba a tarihi, kamar yadda ƙungiyar kula da rikice-rikice ta duniya ta bayyana.

“Wannan barazana ce ga abinci a faɗin duniya, to amma matsalar ta fi ƙamarai ga ƙasashe masu tasowa da ke sayo abincin daga ƙasashen waje.

Kuma saɓanin matsalar abinci da aka fuskanta a baya, a yanzu ana fuskantar matsaloli biyu ne ciki kuwa har da batun tsadar kuɗin dala wanda da shi ne ake cinikayya tsakanin kasashe”.

Majalisar Ɗinkin Duniya ta bayyana cewa duniya ta fuskanci manyan matsalolin tashin farashin abinci guda uku a wannan ƙarni da muke ciki.

Duniya ta fuskanci tashin farashin abinci na farko a wannan ƙarni tsakanin shekarar 2007 zuwa 2008, sai na biyu tsakanin shekarar 2010 zuwa 2012, sai kuma na yanzu wanda annobar Korona da yaƙin Ukraine suka haddasa.

nigeria news(punch)

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Bayan kashe Soja yanzu haka an kama ƴan Daba 398 a Kaduna

Rundunar 'Yan Sandan Jihar Kaduna, ta sanar da kama...

Shettima zai san makomarsa bayan taron APC na ƙasa – Fadar Shugaban Ƙasa

Fadar shugaban ƙasa ta bayyana cewa, sai bayan babban...

Kotu ta ɗaure Matashin da ya shiga ɗakin kwanan Ɗalibai Mata a Kano

Babbar Kotun Shariʼar Musulunci da ke Kofar Kudu a...

Ban gudu daga PDP ba – Namadi Sambo

Tsohon mataimakin shugaban ƙasa, Mohammed Namadi Sambo, ya ƙaryata...

Da yuwar Sojojin mu za su shiga yaƙi don tallafa wa Isra’ila – Trump

Rundunar sojin Isra'ila IDF ta ce ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta kai hari cibiyoyin ƙera nukiliyar Iran

Yayin da aka shiga rana ta shida na yaƙi...

Najeriya za ta kwashe ƴan ƙasarta dake zaune a Iran da Isra’ila

Gwamnatin tarayya ta ce, tana kammala shirye-shiryen gaggawa domin...

Makami mai Linzami ya faɗa kan cibiyar tattara bayanan sirrin Isra’ila

Kafar yaɗa labarai ta gwamnatin Iran ta ce, ƙasar...

Iran ta ƙaddamar da sabbin hare-haren makamai masu linzami kan Isra’ila

Rundunar sojin Isra'ila ta ce, Iran ta ƙaddamar da...

Isra’ila ta na da makaman nukiliya 90

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya dade yana cewa Iran...

Kashe jagoran Iran Ayatullah shi ne kawo ƙarshen rikici – Isra’ila

Firaministan Isra'ila Benjamin Netanyahu ya ce duk wani shiri...

Jerin sunayen masu Fashin Waya 51 da aka kama a Kano

Rundunar ƴansandan Kano, ta fitar da jerin sunayen Mutane...
X whatsapp