fidelitybank

Hatsarin mota ya sa gwamnatin Senegal ta bayar da hutu na kwana 3

Date:

Shugaban ƙasar Senegal Macky Sall ya ayyana hutun kwana uku a ƙasar domin yin makokin mutum 40 da suka mutu bayan wani mummunan hatsarin mota a ƙasar.

Hatsarin wanda ya rutsa da manyan motocin ɗaukar fasinja biyu – waɗanda suka yi taho mu gama da asubahin ranar Lahadi – ya yi sanadin mutuwar mutum 40 tare da jikkata wasu gommai.

Shugaba Mucky Sall ya ce gwamnatin ƙasar za ta yi zaman gaggawa ranar Litinin domin ɗaukar matakan kariya da suka dace, bayan hatsarin wanda ya kasance ɗaya daga cikin munanan hatsarin mota da ƙasar ta taɓa fuskanta a shekarun baya-bayan nan.

Haka kuma a wata mai kama da wannan aƙalla mutum 21 ne suka mutu a lokacin da wata motar bas da ke kan hanyarta ta zuwa birnin Nairobi na ƙasar Kenya ta faɗi jim-kaɗan bayan da ta tsallaka kan iyakar Uganda da Kenya.

Jami’an yan sanda su ce tsananin gudun wuce kima ne ya haddasa hatsarin.

‘Yan sandan Uganda sun ce an samu fiye da haɗura 100 a cikin kwanaki uku a ƙasar cikin sabuwar shekara, lamarin da a cewarsu ya yi sanadin mutuwar mutum 35.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...

Mukarraban gwamnati ba zan lamunci dabi’ar zubar da kima ta ba – Abba

Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya gargaɗi masu...

WAEC ta sake bude shafinta don duba jarabawar bana

Hukumar shirya jarabawar Afirka ta Yamma (WAEC) ta bayyana...

Indonesia za ta gina asibiti dubu biyu ga Falasɗinawa

Indonesia ta sanar da cewa za ta kafa wata...

Lauyan Sowore ya bukaci a sake shi cikin gaggawa

Lauyoyin ffitaccen ɗan gwagwarmayar nan kuma ɗan jarida, Omoyele...

Najeriya da Indiya za su haɗa kai na yaƙi da fataucin miyagun ƙwayoyi

Hukumar hana sha da fatauncin miyagun ƙwayoyi ta Najeriya,...

Jihohi 19 da za a yi kwana 9 a na ruwan sama harda Kano – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta yi hasashen za a shafe kwana...

Tinubu ya mika sakon ta’aziyya bisa rasuwar matar MKO Abiola

Shugaban kasa, Bola Tinubu, ya miƙa saƙon ta'aziyyarsa bisa...

Abubuwan da Kwamiti ya gano a wajen Kwamishina mai murabus na Kano

A ranar Litinin ne kwamitin binciken badaƙalar belin Danwawu,...
X whatsapp