Fasinjoji tara ne ake fargabar sun mutu bayan da motarsu ta kutsa cikin tafkin ruwa na Fada da ke karamar hukumar Gwarzo a jihar Kano.
Kakakin hukumar kashe gobara ta jihar Kano, Saminu Yusuf Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai a ranar Litinin.
Ya ce lamarin ya faru ne a ranar Asabar da misalin karfe 6.45 na yamma.
Ya bayyana cewa hatsarin ya faru ne a lokacin da wata mota kirar Golf mai dauke da fasinjoji 12 ta taho daga Kano ta nufi jihar Katsina.
A cewar sanarwar “Lamarin ya faru ne a ranar Asabar, 19 ga Nuwamba, 2022. Hukumar kashe gobara ta jihar ta samu kiran gaggawa ta hannun Ali Mai Faci, cewa da misalin karfe 18:45, wata mota dauke da fasinjoji goma sha biyu ta kutsa cikin karamar hukumar Fada dam Gwarzo.
“Hatsarin ya faru ne a sakamakon wata matsala da wata mota ta tsaya a tsakiyar titi ba tare da yiwa masu ababen hawa umarnin yin taka tsantsan ba.”
Ya ce mutane tara ne suka mutu yayin da aka ceto mutane uku.