fidelitybank

Hatsarin kwale-kwale ya lashe rayukan mutane 936 a Najeriya

Date:

Aƙalla mutum 936 ne suka mutu a hatsarin jirgin ruwa daba-daban da suka faru a Najeriya cikin shekara uku.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, ƙarancin hanyoyin cikin ruwa marasa cunkushewa da yayi da kuma ɗaukar fasinjoji da suka wuce iyaka na cikin matsalolin da ke janyo wannan lamari.

Hakan ya sa a ranar Talata Shugaba Bola Tinubu ya ba da umarnin gudanar da bincike kan yawan kifewar kwale-kwale a Najeriya da yake neman zama ruwan dare.

Masana dai na ta bayar da shawara cewa ya kamata mahukunta su ɗauki matakin da ya wuce na furtawa da fatar baki kawai a gani a aikace don a shawo kan wannan matsala.

Sun kuma bayar da shawara kan cewa kamata ya yi a maye gurbin kwale-kwalen da ake da su na gargajiya da na zamani, domin ci gaba da sufuri da su.

A Najeriya dai sufuri ta hanyar jirgin ruwa na gudana ne a hannun mazauna ƙauyukan da ruwan yake, abu ne da gwamnati ba ta mayar da hankali a kai ba, wanda hakan ya sabawa ka’idar aikin da aka shimfiɗa a duniya.

Hatsarin da ya faru a makon jiya ya yi sanadin mutuwar sama da mutum 20, ya janyo wa hukumomin da ke lura da sufurin jiragen ruwa suka na rashin mayar da hankali kan abin da ke gudana arewacin Najeriya da Allah ya albarkanta da tafkuna da kuma ƙoramu.

Sai dai kullum hukumomi na iƙirarin suna iya ƙoƙarinsu domin daƙile wannan matsala.

nigerian 
news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp