Shugabar ƙasar Tanzaniya Samia Suluhu za ta gudanar da taron gaggawa da ministocin ƙasar domin tattauna batun faduwar jirgin saman da ya auku a makon da ya gabata tare da kashe mutum 19.
Jirgin saman fasinjan ya faɗi ne cikin tekun Victoria ranar shida ga watan Nuwamba, a lokacin da ya yi yunƙurin saukar gaggawa.
Masu bincike daga kamfanin jirgin da ƙwararru daga Faransa na garin da lamarin ya auku domin gano musabbabin faruwar hatsarin.
Jirgin saman mallakin Precision Air, kamfanin jirgin sama mai zaman kansa mafi girma a Tanzaniya, wanda ke zirga-zirga a ƙasar tun shekarar 1994.