fidelitybank

Hatsarin hanyar Bauchi ya kashe mutane biyu

Date:

Mutane biyu ne suka mutu a wani hatsarin mota daya tilo da ya afku a hanyar Darazo-Dukku a jihar Bauchi, yayin da wasu biyar suka samu raunuka daban-daban a hadarin da yammacin ranar Talata.

Rahoton da kwamandan hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi Yusuf Abdullahi ya fitar ya tabbatar da hakan.

A cewar rahoton, hatsarin daya tilo da wata farar mota kirar Toyota Hiace, mai lamba DKA 127 XT, ta afku ne a kauyen Kahun da misalin karfe 6:36 na yamma, inda ya kara da cewa, an sanar da jami’an hukumar faruwar hatsarin ne da karfe 6:40 na yamma, a yayin da sun dauki jami’an FRSC na mintuna 20 don isa wurin da hatsarin ya afku, mai tazarar kilomita 14 daga sansaninsu domin gudanar da aikin ceto.

Rahoton ya ce motar Toyota Hiace na dauke da fasinjoji 14, dukkansu maza ne, a daidai lokacin da hadarin ya afku.

Yayin da yake danganta musabbabin hatsarin da fashewar tayoyi, rahoton ya kara da cewa wadanda suka jikkata sun samu raunuka da suka hada da rauni da kai da karaya.

Ya kara da cewa an ajiye gawarwakin mutanen biyu a dakin ajiyar gawa na babban asibitin Darazo, yayin da wadanda suka jikkata ke karbar kulawa a asibiti daya.

nnnnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Hogan ya mutu bisa cutar gazawar koda

An bayyana cikakkun bayanai game da mutuwar É—an wasan...

Sojoji sun kashe rikaken dan Bindiga Dan Dari Biyar a Sokoto

Dakarun Operation FANSAR YANMA sun yi nasarar fatattakar wani...

An kashe utane 30 a yakin Thailand da Cambodia

An shiga kwana na uku na faÉ—an kan iyaka...

Ba mu Æ™ayyade shekarun shiga Æ™aramar sakandare JSS1 – Ma’aikatar Ilimi

Ma'aikatar Ilimi a Najeriya ta musanta rahoton da wasu...

Ido da Ido na ga yadda Sojojin Isra’ila ke kashe Falasdinawa – Tsohon Sojin Amurka

Wani tsohon sojan Amurk ya ce, ya ga yadda...

‘Yan majalisar Birtaniya 220 na neman Æ™asar ta amice da Æ™asar FalasÉ—inu

'Yan majalisar Birtaniya 220 sun nemi gwamnatin ƙasar ta...

Buhari yaki karbar kyautar Agogon lu’u-lu’u da jirgin sama – Garba Shehu

Mai magana da yawun tsohon Shugaban Najeriya Muhammad Buhari,...

An kama wanda ya kashe tsohuwar Matarsa a Jigawa

Ƴansandan Jihar Jigawa sun ce, sun kama wani mutum...

Fadar shugaban kasa ta mayar da martani kan Kwankwaso

Fadar shugaban kasa, ta mayar wa tsohon gwamnan Kano...

Barau FC ta naÉ—a Ladan Bosso sabon kocinta

Ƙungiyar ƙwallon ƙafa ta Barau FC ta sanar da...

Am fara dawo da ‘yan Najeriya daga Afrika ta Tsakiya

Hukumomi a Najeriya sun ce, sun fara ƙoƙarin mayar...

G-Fresh da Hamisu Breaker sun samu gurbi kurkuku bayan sun watsa Naira

Babbar kotun tarayya da ke jihar Kano É—aure shahararrun...
X whatsapp