fidelitybank

Hatsari ya hallaka matafiya 25 yayin da 53 suka jikkata a Kano

Date:

Hukumar kiyaye haddura ta kasa FRSC reshen jihar Kano, ta tabbatar da mutuwar matafiya 25, yayin da wasu 53 suka samu raunuka a wani hatsarin mota da ya afku a safiyar yau.

Lamarin ya faru ne a kasuwar duniya ta Dangwaro da ke unguwar babban birnin Kano.

An ce matafiya an yi lodin su ne a cikin wata tirela wadda ita ma dauke da shanu ta nufi Kudancin Najeriya daga Maiduguri.

Sai dai tirelar ta yi karo da wata motar kuma ta yi ta’adi.

Kwamandan hukumar FRSC reshen jihar, Ibrahim Abdullahi ya tabbatar da faruwar lamarin a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai ranar Litinin a Kano.

Ya ce hadarin ya rutsa da wata tirela (IVECO) mai lamba XA 311 ZB.

“Mun samu kira da misalin karfe 03:15 na safiyar ranar 1 ga Yuli, 2024. Da samun labarin, mun aika da jami’an mu da motar mu cikin gaggawa zuwa wurin da lamarin ya faru domin ceto wadanda abin ya shafa da karfe 03:30 na safe,” in ji Ibrahim.

Kwamandan sashin ya ce hatsarin ya afku ne sakamakon wuce gona da iri, tukin mota mai hatsari da kuma wuce gona da iri wanda hakan ya janyo rasa natsuwa.

Ya kuma bayyana cewa a yayin aikin ceto kayayyakin da aka kwato sun hada da babura shida, wayoyin hannu guda goma, dabbobi (awaki da raguna), masara da kudi N400,000.

Abdullahi ya ce duk kayayyakin da aka kwato suna hannun ‘yan sanda.

“Ba tare da bata lokaci ba aka kai dukkan wadanda abin ya shafa asibitin kwararru na Murtala Muhammed Kano domin samun kulawar gaggawa.

“Likitocin da ke bakin aiki sun tabbatar da mutuwar mutane 25 daga cikin wadanda abin ya shafa,” in ji shi.

Ya gargadi masu ababen hawa kan rashin tsaro na safarar dabbobi, kayayyaki, tare da mutane.

breaking news in nigeria today 2022

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp