Akalla mutum 22 aka tabbatar sun mutu a wani mummunan hatsarin mota da ya faru a arewacin kasar Masar.
Motar kirar bas ta saki hanya a garin Aga da ke kusa da gabar Kogin Nilu. Mutum 35 ne ke cikin motar lokacin da aka yi hatsarin.
Tuni aka kama direban motar, wanda shi ma ya ji mummunan rauni, ana zarginsa da tukin ganganci da gudu fiye da kima. An kuma yi masa gwajin shan mugayen ƙwayoyi amma sakamako ya nuna ba shi da alaƙa da su.
Wasu da suka tsira daga hatsarin sun shaida wa jami’an tsaro cewa direban yana amsa waya ne a daidai lokacin da motar ta kuÉ“uce masa.