Wasu matasa masu yi wa kasa hidima su biyar sun rasu a kan hanyarsu ta komawa gida bayan kammala samun horo a Karamar Hukumar Fika ta Jihar Yobe.
Matasan sun rasu ne a wani hatsarin mota da ya ritsa da su a lokacin da su ke kan hanyarsu ta komawa garuruwansu a Jihar Yobe, bayan sun kammala samun horon kwana 21 a sansanin masu yi wa kasa hidima ta Jihar Taraba.
Wani ganau, Sule Audu, ya ce, lamarin ya auku ne ranar Talata da yamma inda motar hayar da ta dauko matasan ta yi taho-mu-maga da wata tarakta.
Ya ce kuma ce, bayan hatsarin, an garzaya da matasan zuwa asibiti a garin Fika, inda wasunsu suka ce ga garinku nan.
Wadanda ke cikin Rukunin C kashi na II na masu yi wa kasa hidima, takwarorinsu sun bayyana matukar kaduwa da samun labarin rasuwarsu.
Sauran wadanda suka samu raunin kuma an kai su Asibitin Kwararru da ke Damaturu.
Mai magana da yawun Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) Hussaini Haruna, ya tabbatar wa Aminiya da aukuwar hatsarin, sai dai bai bayyana wurin da abin ya faru ba.
Aminiya ta gano cewa daga cikin wadanda suka rasun akwai Ali Muhammad Ahmad, wanda ya kammala karatun Digirin farko a fannin Kemistiri daga Jami’ar Tarayya da ke Dutse; Audu Sani Tatata, (Kemistiri daga Jami’ar Maiduguri), dukkansu ’yan asalin Potiskum; Auwal Hamisu Bashari, (B.A (Ed) Islamic Education) daga Jami’ar Jihar Yobe, dan asalin Nguru; da sauransu.