fidelitybank

Hatsari: An yi wa kasa hidima sun yi taho mu gama da wata mota

Date:

Wasu matasa masu yi wa kasa hidima su biyar sun rasu a kan hanyarsu ta komawa gida bayan kammala samun horo a Karamar Hukumar Fika ta Jihar Yobe.

Matasan sun rasu ne a wani hatsarin mota da ya ritsa da su a lokacin da su ke kan hanyarsu ta komawa garuruwansu a Jihar Yobe, bayan sun kammala samun horon kwana 21 a sansanin masu yi wa kasa hidima ta Jihar Taraba.

Wani ganau, Sule Audu, ya ce, lamarin ya auku ne ranar Talata da yamma inda motar hayar da ta dauko matasan ta yi taho-mu-maga da wata tarakta.

Ya ce kuma ce, bayan hatsarin, an garzaya da matasan zuwa asibiti a garin Fika, inda wasunsu suka ce ga garinku nan.

Wadanda ke cikin Rukunin C kashi na II na masu yi wa kasa hidima, takwarorinsu sun bayyana matukar kaduwa da samun labarin rasuwarsu.

Sauran wadanda suka samu raunin kuma an kai su Asibitin Kwararru da ke Damaturu.

Mai magana da yawun Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) Hussaini Haruna, ya tabbatar wa Aminiya da aukuwar hatsarin, sai dai bai bayyana wurin da abin ya faru ba.

Aminiya ta gano cewa daga cikin wadanda suka rasun akwai Ali Muhammad Ahmad, wanda ya kammala karatun Digirin farko a fannin Kemistiri daga Jami’ar Tarayya da ke Dutse; Audu Sani Tatata, (Kemistiri daga Jami’ar Maiduguri), dukkansu ’yan asalin Potiskum; Auwal Hamisu Bashari, (B.A (Ed) Islamic Education) daga Jami’ar Jihar Yobe, dan asalin Nguru; da sauransu.

 

latest news 
in nigeria today 2021 punch

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An kashe Æ´an Boko Haram biyar a Borno

Dakarun sojin Najeriya haɗe da wasu maharba sun daƙile...

Farashin Shinkafa zai cigaba da sauka – BUA

Shugaban rukunin kamfanonin BUA, Abdul Samad Rabiu, ya alƙawarta...

An kashe mutane 10 a wani sabon rikici da ya ɓarke a Filato

Aƙalla mutabe 10 ne aka kashe tare da sace...

Duk da sauƙin da aka samu har yanzu Abuja na fuskantar hauhawar farashi

Duk da cewa hukumar ƙididdiga ta ƙasa NBS, ta...

Hauhawar farashi ya ragu da kaso 23.71 a Najeriya – NBS

An samu raguwar hauhawar farashin kayayyaki a Najeriya daga...

Fiye da mutane 100 Makiyaya aka kashe a Jos

An ruwaito cewa an kashe wani makiyayi guda da...

Tinubu ka kori shugaban JAMB – Sowore

Dan siyasa mai fafutuka, Omoyele Sowore, ya yi kira...

Majalisa ta yi watsi da ƙudirin karɓa-karɓa

Majalisar wakilai ta yi watsi da wani ƙudirin doka...

Labarin mu na kaiwa Ƴan Bindiga abinci Æ™arya ne – Ƴansanda

Rundunar Æ´ansandan Najeriya ta musanta rahotannin da ake yaÉ—awa...

Ba za mu yarda mu mutu a cikin PDP ba shi yasa muka koma APC – Sanatoci

Sanatocin Najeriya uku da suka fito daga jihar Kebbi,...

Sojoji sun tarwatsa wajen da ake hakar man fetur ba bisa ka’ida ba a Rivers

Rundunar Sojin Ruwa ta Najeriya, NNS, Pathfinder, ta tarwatsa...

Dan Tinubu Seyi da sauran ‘yan Siyasa sun fara neman kujerar gwamnan Legas

Siyasar Legas na kara ruruwa na neman maye gurbin...
X whatsapp