fidelitybank

Hatsari: An yi wa kasa hidima sun yi taho mu gama da wata mota

Date:

Wasu matasa masu yi wa kasa hidima su biyar sun rasu a kan hanyarsu ta komawa gida bayan kammala samun horo a Karamar Hukumar Fika ta Jihar Yobe.

Matasan sun rasu ne a wani hatsarin mota da ya ritsa da su a lokacin da su ke kan hanyarsu ta komawa garuruwansu a Jihar Yobe, bayan sun kammala samun horon kwana 21 a sansanin masu yi wa kasa hidima ta Jihar Taraba.

Wani ganau, Sule Audu, ya ce, lamarin ya auku ne ranar Talata da yamma inda motar hayar da ta dauko matasan ta yi taho-mu-maga da wata tarakta.

Ya ce kuma ce, bayan hatsarin, an garzaya da matasan zuwa asibiti a garin Fika, inda wasunsu suka ce ga garinku nan.

Wadanda ke cikin Rukunin C kashi na II na masu yi wa kasa hidima, takwarorinsu sun bayyana matukar kaduwa da samun labarin rasuwarsu.

Sauran wadanda suka samu raunin kuma an kai su Asibitin Kwararru da ke Damaturu.

Mai magana da yawun Hukumar Kiyaye Haddura ta Kasa (FRSC) Hussaini Haruna, ya tabbatar wa Aminiya da aukuwar hatsarin, sai dai bai bayyana wurin da abin ya faru ba.

Aminiya ta gano cewa daga cikin wadanda suka rasun akwai Ali Muhammad Ahmad, wanda ya kammala karatun Digirin farko a fannin Kemistiri daga Jami’ar Tarayya da ke Dutse; Audu Sani Tatata, (Kemistiri daga Jami’ar Maiduguri), dukkansu ’yan asalin Potiskum; Auwal Hamisu Bashari, (B.A (Ed) Islamic Education) daga Jami’ar Jihar Yobe, dan asalin Nguru; da sauransu.

 

yola news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Yunwa na kara tsananta a arewa maso gabashin Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta Red cross (ICRC) ta bayyana yadda...

Ba zan taba watsawa Tinubu kasa a ido ba – IBB

ÆŠan tsohon shugaban kasa, Janar Ibrahim Badamasi Babangida, wato...

Natasha kar ki kuskura ki dawo aiki – Majalisa

Majalisar Dattijai ta buƙaci Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta dakatar...

Za a yi ruwan sama da iska mai Æ™arfi a jihohi harda Kano – NiMET

Hukumar kula da yanayi ta Najeriya (NiMET) ta fitar...

Obi da El-Rufa’i za su koma jam’iyyar mu a hukumance – ADC

Sakataren yada labarai na rikon kwarya na jam’iyyar African...

Za mu tattauna da tarayyar Turai a kan Nukiliyarmu – Iran

Iran ta tabbatar cewa za ta gudanar da tattaunawa...

Mu na gargadin Isra’ila kan korar al’ummar Gaza daga yankin su – MDD

Hukumar kula da ayyukan jin-ƙai ta Majalisar Ɗinkin Duniya...

Rikici ya kuma balle a Syria

Ƙungiyoyin kare haƙƙin dan'adam sun ce, wani sabon rikici...

Tsofaffin ‘Yansanda na da ‘yancin yin zanga-zanga – A Cewar Amnesty

Ƙungiyar Amnesty International ta ce tsofaffin ƴansandan Najeriya girmamawa...

Buhari ya yi wa Najeriya hidimar da ba za a manta da shi ba – António Guterres

Babban Sakatare na Majalisar Ɗinkin Duniya (MDD) António Guterres...

Binani ta koma jam’iyyar haÉ—aka ta ADC

'Yartakarar gwamnan jihar Adamawa a zaɓen 2023, Sanata Aishatu...

A Talata zan koma aiki na a majalisa – Natasha

Yar majalisar Dattawa, Sanata Natasha Akpoti, ta ci alwashin...
X whatsapp