Wasu ‘yan bindiga da ake zargin ‘yan fashin daji ne sun hallaka Baturan ‘yan sandan (DPO), yayin wani hari a garin Jibiya na Jihar Katsina daren Talata.
DSP A. A. Rano wanda shi ne DPO na Jibiya, ya rasa ransa ne lokacin da ‘yan fashin suka afka wa garin suna harbe-harbe kan mai uwa dawabi.
Maharan sun kuma harbi wani soja a ƙafa kuma daga baya ya rasu, kazalika sun harbi wani kwamanda na soji da yanzu haka ya na asibiti a kwance.
BBC ta tabbatar da labarin daga sahihan majiyoyi da dama, bayan da muka kira mai magana da yawun Æ´an sandan jihar Katsinan Gambo Isa amma bai É—auki waya ba.
Amma an ga wani saÆ™o da SP Gambo Isa ya wallafa na ta’aziyyar marigayin a wani zaure na WhatsApp, sannan majiyoyi daga Jibiyan sun tabbatar SP Gambo Isa ya je wurin da abin ya faru.
Wani mazaunin yankin ya faÉ—a wa BBC Hausa cewa, lamarin ya faru a kan idonsa, yayin da tawagar haÉ—in gwiwar jami’an tsaro ta ‘yan sanda da sojoji suka fafata da ‘yan bindigar kafin daga bisani su gudu cikin daji da mutanen da suka yi garkuwa da su.
Maharan sun sace wata mata da diyarta wanda a garin ceto su ne aka harbe DPO É—in.
A ranar Litinin da dare ma wasu ‘yan fashi sun kashe mutum 12 tare da kama wasu da Æ™ona gidajen garin Guga na Ƙaramar Hukumar Bakori ta Katsina.