fidelitybank

Harin Yan Bindiga ya hallaka mutane da dama a Taraba

Date:

Gwamnan jihar Taraba, Agbu Kefas, ya yi Alla-wadai da harin da ƴanbindiga suka kai kan al’ummomin Munga Lelau a karamar hukumar Karim Lamido na jihar, abin da ya janyo mutuwar mutane da ba a san adadinsu ba.

Ƴanbindigar sun kai harin ne a lokacin da mutane ke komawa gida daga gonakinsu.

Lamarin ya afku da yammacin ranar Juma’a, makonni kalilan bayan wasu da ake zargin ƴanbindiga sun kashe wasu manoma biyu a yankin Bandawa na jihar.

Gwamna Kefas ya ce ba za a lamunci kai irin waɗannan hare-hare ba, inda ya ce suna mayar da jihar baya maimakon ci gaba.

Ya gargaɗi masu kai harin da cewa za su ɗanɗani kuɗarsu.

Ya kuma ƙara nanata cewa yana duk mai yiwuwa domin tsare jihar daga hare-hare da ake kai wa.

Ya ƙara da cewa akwai buƙakatar haɗa-kai tsakanin al’umma da jami’an tsaro, musamman wajen bayar da bayanan da suka kamata.

nnn

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp