Wani tsohon mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Malam Ibrahim Wakkala Linan, ya samu munanan raunuka, sakamakon harin da ‘yan ta’adda suka kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna, kuma yanzu haka an kwantar da shi a wani asibitin sojoji dake jihar Kaduna.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Malam Yusuf Idris Gusau ya tabbatar da hakan.
A cewarsa, tun farko ‘yan ta’addar sun yi garkuwa da tsohon Mataimakin Gwamnan a yayin harin, amma hadin gwiwar jami’an tsaro na farin kaya (DSS) da jami’an soji sun ceto shi a wani artabu da ‘yan ta’addan.
“Da farko an yi garkuwa da ni amma tare da hadin gwiwar sojoji da jami’an DSS suka kubutar da ni, kuma a lokacin da ake gudanar da aikin, ba samu raunuka iri-iri a kafata sakamakon gumurzun da suka yi da bindiga,” ya kara da cewa.
Duk da haka, yana karbar magani sosai a asibitin sojoji da ke jihar Kaduna.
DAILY POST ta tattaro cewa an saki hoton tsohon mataimakin gwamnan jihar Zamfara, Ibrahim Wakkala bayan harin.
An kuma bayyana cewa, jirgin na jigilar daruruwan fasinjoji daga Abuja zuwa Kaduna, kuma wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton ‘yan ta’adda ne da suka yi kaurin suna wajen kai farmaki a tsakanin Katari da Rijana ta jihar Kaduna, sun kai farmaki.