fidelitybank

Harin jirgin yaƙin sojin saman Nijeriya ya hallaka wani kwamandan ISWAP

Date:

 

Jirgin yaƙin Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa, NAF, Super Tucano da ke karkashin Operation Hadin Kai ya hallaka kwamandojin ISWAP da dama da sauran ‘yan ta’adda a Kirta Wulgo.

Jaridar PRNigeria ta tattaro bayanai cewa, an kashe babban kwamandan ISWAP, Mallam Ari, wanda ke kula da Kirta Wulgo, da wasu sojojin hayar da su ka dauko da ga ƙasashen waje da ke haɗa abubuwan fashewa, IED, ga ‘yan ta’addar, a yayin farmakin da jiragen yaƙin suka kai musu.

Wani babban jami’in leken asiri na soji ya ce an ba da izinin kai hare-haren ne bayan bayanan sirri sun gano sama da ‘yan ta’adda 40 ne suka samu wajen zama a yankin Arewa maso Gabashin Kirta Wulgo, kusa da wurin da ake zargin ISWAP ɗin ta kafa tutar ta.

“An kuma ga wasu dauke da makamai a kusa da wani gini na ƙwarya-ƙwarya da ke kusa, wanda hakan wata alama ce da ke nuna cewa ginin an yi shi ne domin haɗa manyan hare-hare.

“Bayan harin da aka kai ta sama, an ga wasu daga cikin ‘yan ta’addan da suka tsira da ransu suna kokarin kashe gobarar da ta tashi yayin da wasu kuma suka tsere.

“Hakika, gine-ginen sun kone sosai kuma an lalata su a yankin.”

“An kashe mayakan ISWAP da dama a harin da aka kai ta sama ciki har da wani Malam Ari wanda aka bayyana sunansa da Fiya na Kirta Wulgo.”

Fiya lakabi ne na matsayi na biyu a tsarin tsarin muƙaman ‘yan ta’addan.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ta NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya tabbatar da cewa rundunar ta kai wasu hare-hare a wasu yankunan da ke kusa da Kirta Wulgo, amma ta yi shiru kan adadin wadanda suka mutu ko kuma su wanene.

Kwanan nan shugabannin ISWAP sun yi sauye-sauyen mukamai saboda asarar wasu manyan mambobinta da aka kashe musamman ta hanyar kai hare-hare ta sama da jiragen NAF suka yi.

daily post newspaper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Dakarun sojin ruwa a Najeriya sun yi kaɗan wajen tsaron ƙasa – Emmanuel Ogalla

Babban hafsan sojin ruwa na Najeriya ya ce dakarunsa...

Juma’a da Litinin ranakun hutun Sallar Layya – Gwamnati

Gwamnatin Tarayya ta ayyana ranakun Juma'a da Liitnin masu...

Gwamnatin Neja zai haɗa kai da matatar Ɗangote wajen haƙo ɗanyen man fetur

Gwamnan jihar Neja, Umar Bago, ya nemi aikin haɗin...

Tchiani ya zargi Najeriya, Faransa, China da Amurka wajen cutar da Nijar

Shugaban sojin Nijar, Janar Abdourahmane Tchiani, ya zargi Najeriya...

An ceto yara 12 da aka yi safararsu a jihar Abia

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta ce jami'anta sun samu...

A na neman kusan Mutane 400 da suka ɓace a ambaliyar Neja

A na ci gaba da ayyukan ceto bayan ambaliyar...

Mun bayar da hutu ranar Litinin bisa jimamin mutuwar ƴan Wasa – Gwamnatin Kano

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya ayyana ranar...

Tun farko na shaida wa Tinubu ba zan zaɓe shi ba – Amaechi

Tsohon ministan sufuri na Najeriya, Rotimi Amaechi ya ce...

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...
X whatsapp