fidelitybank

Harin jirgin yaƙin sojin saman Nijeriya ya hallaka wani kwamandan ISWAP

Date:

 

Jirgin yaƙin Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa, NAF, Super Tucano da ke karkashin Operation Hadin Kai ya hallaka kwamandojin ISWAP da dama da sauran ‘yan ta’adda a Kirta Wulgo.

Jaridar PRNigeria ta tattaro bayanai cewa, an kashe babban kwamandan ISWAP, Mallam Ari, wanda ke kula da Kirta Wulgo, da wasu sojojin hayar da su ka dauko da ga ƙasashen waje da ke haɗa abubuwan fashewa, IED, ga ‘yan ta’addar, a yayin farmakin da jiragen yaƙin suka kai musu.

Wani babban jami’in leken asiri na soji ya ce an ba da izinin kai hare-haren ne bayan bayanan sirri sun gano sama da ‘yan ta’adda 40 ne suka samu wajen zama a yankin Arewa maso Gabashin Kirta Wulgo, kusa da wurin da ake zargin ISWAP ɗin ta kafa tutar ta.

“An kuma ga wasu dauke da makamai a kusa da wani gini na ƙwarya-ƙwarya da ke kusa, wanda hakan wata alama ce da ke nuna cewa ginin an yi shi ne domin haɗa manyan hare-hare.

“Bayan harin da aka kai ta sama, an ga wasu daga cikin ‘yan ta’addan da suka tsira da ransu suna kokarin kashe gobarar da ta tashi yayin da wasu kuma suka tsere.

“Hakika, gine-ginen sun kone sosai kuma an lalata su a yankin.”

“An kashe mayakan ISWAP da dama a harin da aka kai ta sama ciki har da wani Malam Ari wanda aka bayyana sunansa da Fiya na Kirta Wulgo.”

Fiya lakabi ne na matsayi na biyu a tsarin tsarin muƙaman ‘yan ta’addan.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ta NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya tabbatar da cewa rundunar ta kai wasu hare-hare a wasu yankunan da ke kusa da Kirta Wulgo, amma ta yi shiru kan adadin wadanda suka mutu ko kuma su wanene.

Kwanan nan shugabannin ISWAP sun yi sauye-sauyen mukamai saboda asarar wasu manyan mambobinta da aka kashe musamman ta hanyar kai hare-hare ta sama da jiragen NAF suka yi.

spw

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Rundunar sojin ruwa za ta kafa sansani a Kebbi

Rundunar sojin ruwan Najeriya ta bayyana aniyar kafa sansaninta...

Za afara rijistar masu zabe a Najeriya – INEC

Hukumar zaɓe ta INEC, ta ce, nan gaba cikin...

Ma’aikatan Jinya sun dakatar da yajin aiki a Najeriya

Ministan lafiya a Najeriya ya ce, ma'aikatan jinya da...

Izak ya na ɗaukar horo bayan ya dage sai ya koma Liverpool

Ɗanwasan gab ana Newcastle Alexander Isak na can yana...

Masu tsaigunta wa ƴan Bindiga ne ke haddasa kashe-kashe – Gwamnan Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta ce masu tsegunta wa ƴanbindiga...

Gwamnoni ku yi wa mutanen ƙauyika da karkara ayyuka – Tinubu

Shugaba Bola Tinubu, ya buƙaci gwamnonin ƙasar nan su...

Dino Melaye ya gudu daga PDP ya faɗa ADC

Tsohon ɗan jamalisar dattawa mai wakiltar Kogi ta Yamma,...

Isra’ila na zargin Canada da goyon bayan Hamas – Netanyahu

Isra'ila ta zargi Canada da taimaka wa Hamas bayan...

Rashin tallafin agaji ka iya dawo da Boko Haram a Najeriya – MDD

Hukumar Samar da Abinci ta Majalisar Dinkin Duniya ta...

Yin gini a kan hanyoyin ruwa ne ya janyo ambaliyar Maiduguri – NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa da Najeriya NEMA ta...

Amnesty ta yi Allah wadai da tsare Sultan kan bidiyon lafiyar Tinubu

Ƙungiyar kare haƙƙin bil'adama ta Amnesty International ta yi...

Dalilin da ya sa na gana da Tinubu – Kofa

Ɗan majalisar tarayyar mai wakilitar Kiru da Bebeji daga...
X whatsapp