fidelitybank

Harin jirgin yaƙin sojin saman Nijeriya ya hallaka wani kwamandan ISWAP

Date:

 

Jirgin yaƙin Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa, NAF, Super Tucano da ke karkashin Operation Hadin Kai ya hallaka kwamandojin ISWAP da dama da sauran ‘yan ta’adda a Kirta Wulgo.

Jaridar PRNigeria ta tattaro bayanai cewa, an kashe babban kwamandan ISWAP, Mallam Ari, wanda ke kula da Kirta Wulgo, da wasu sojojin hayar da su ka dauko da ga ƙasashen waje da ke haɗa abubuwan fashewa, IED, ga ‘yan ta’addar, a yayin farmakin da jiragen yaƙin suka kai musu.

Wani babban jami’in leken asiri na soji ya ce an ba da izinin kai hare-haren ne bayan bayanan sirri sun gano sama da ‘yan ta’adda 40 ne suka samu wajen zama a yankin Arewa maso Gabashin Kirta Wulgo, kusa da wurin da ake zargin ISWAP ɗin ta kafa tutar ta.

“An kuma ga wasu dauke da makamai a kusa da wani gini na ƙwarya-ƙwarya da ke kusa, wanda hakan wata alama ce da ke nuna cewa ginin an yi shi ne domin haɗa manyan hare-hare.

“Bayan harin da aka kai ta sama, an ga wasu daga cikin ‘yan ta’addan da suka tsira da ransu suna kokarin kashe gobarar da ta tashi yayin da wasu kuma suka tsere.

“Hakika, gine-ginen sun kone sosai kuma an lalata su a yankin.”

“An kashe mayakan ISWAP da dama a harin da aka kai ta sama ciki har da wani Malam Ari wanda aka bayyana sunansa da Fiya na Kirta Wulgo.”

Fiya lakabi ne na matsayi na biyu a tsarin tsarin muƙaman ‘yan ta’addan.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ta NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya tabbatar da cewa rundunar ta kai wasu hare-hare a wasu yankunan da ke kusa da Kirta Wulgo, amma ta yi shiru kan adadin wadanda suka mutu ko kuma su wanene.

Kwanan nan shugabannin ISWAP sun yi sauye-sauyen mukamai saboda asarar wasu manyan mambobinta da aka kashe musamman ta hanyar kai hare-hare ta sama da jiragen NAF suka yi.

assu news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp