fidelitybank

Harin jirgin yaƙin sojin saman Nijeriya ya hallaka wani kwamandan ISWAP

Date:

 

Jirgin yaƙin Rundunar Sojin Sama ta Ƙasa, NAF, Super Tucano da ke karkashin Operation Hadin Kai ya hallaka kwamandojin ISWAP da dama da sauran ‘yan ta’adda a Kirta Wulgo.

Jaridar PRNigeria ta tattaro bayanai cewa, an kashe babban kwamandan ISWAP, Mallam Ari, wanda ke kula da Kirta Wulgo, da wasu sojojin hayar da su ka dauko da ga ƙasashen waje da ke haɗa abubuwan fashewa, IED, ga ‘yan ta’addar, a yayin farmakin da jiragen yaƙin suka kai musu.

Wani babban jami’in leken asiri na soji ya ce an ba da izinin kai hare-haren ne bayan bayanan sirri sun gano sama da ‘yan ta’adda 40 ne suka samu wajen zama a yankin Arewa maso Gabashin Kirta Wulgo, kusa da wurin da ake zargin ISWAP ɗin ta kafa tutar ta.

“An kuma ga wasu dauke da makamai a kusa da wani gini na ƙwarya-ƙwarya da ke kusa, wanda hakan wata alama ce da ke nuna cewa ginin an yi shi ne domin haɗa manyan hare-hare.

“Bayan harin da aka kai ta sama, an ga wasu daga cikin ‘yan ta’addan da suka tsira da ransu suna kokarin kashe gobarar da ta tashi yayin da wasu kuma suka tsere.

“Hakika, gine-ginen sun kone sosai kuma an lalata su a yankin.”

“An kashe mayakan ISWAP da dama a harin da aka kai ta sama ciki har da wani Malam Ari wanda aka bayyana sunansa da Fiya na Kirta Wulgo.”

Fiya lakabi ne na matsayi na biyu a tsarin tsarin muƙaman ‘yan ta’addan.

A lokacin da aka tuntubi kakakin rundunar ta NAF, Air Commodore Edward Gabkwet, ya tabbatar da cewa rundunar ta kai wasu hare-hare a wasu yankunan da ke kusa da Kirta Wulgo, amma ta yi shiru kan adadin wadanda suka mutu ko kuma su wanene.

Kwanan nan shugabannin ISWAP sun yi sauye-sauyen mukamai saboda asarar wasu manyan mambobinta da aka kashe musamman ta hanyar kai hare-hare ta sama da jiragen NAF suka yi.

nnn.ng

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Fernandes na duba yiwuwar barin Man Utd zuwa Al-Hilal

Bruno Fernandes na duba yiwuwar ficewa daga Manchester United...

Gwamnatin Tinubu ta jefa al’umma fiye da miliyan 150 cikin tsananin talauci – NLC

A daidai lokacin da gwamnatin shugaban Najeriya Bola Ahmed...

Sojoji sun ce sun hallaka ƴan Ta’adda 60 a jihar Borno

Dakarun sojijin Operation Haɗin-Kai sun ce sun kashe ƴan...

Zan cigaba da jajircewa a kan rantsuwar da na yi ta kujera ta – Fubara

Gwamnan jihar Ribas da aka dakatar, Sim Fubara, ya...

Ambaliya ya kashe Mutane a jihar Neja

Wasu rahotanni sun bayyana cewa, mutane da dama sun...

Kotu ta tabbatar da nasarar Gwamnan Edo

Kotun daukaka kara da ke Abuja ta amince da...

An kashe aƙalla mutum 10,217 a mulkin Tinubu – Amnesty

Wani bincike da ƙungiyar Amnesty International ta fitar kwanan...

Gwamnati ba ta tausayin Talaka – Atiku

Ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar PDP a zaben...

Elon Musk ya ajiye aikin da Trump ya naɗa shi

Hamshaƙin attajirin nan Elon Musk ya sanarda aniyarsa ta...

‘Yar Najeriya ta haihuwa a aikin Hajjin bana

Wata mata da ta je aikin hajji daga jihar...

Rashin nadi da jinkiri ne ya kawo rashin nasarar mu a kakar 2024/2025 – Kano Pillars

Kungiyar Kano Pillars ta yi imanin cewa jinkirin shirye-shiryen...
X whatsapp