Hare-haren da ‘yan ta’addan suka kai kan titin jirgin kasa da filin jirgin sama a jihar Kaduna a baya-bayan nan ya janyo suka ga Gwamnatin Tarayya kan gazawarta na shawo kan lamarin.
Debo Ologunagba, Sakataren Yada Labarai na Jam’iyyar PDP na kasa a ranar Laraba ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta mika kasar ga ‘yan ta’adda.
Hakan dai ya biyo bayan wani harin kwantan bauna da ‘yan ta’adda suka yi wa wani jirgin kasa kan hanyar Abuja zuwa Kaduna, inda suka kashe ‘yan Najeriya da dama tare da yin awon gaba da wasu da dama, a wani samame da ya dauki tsawon sa’a guda ana yi, a ranar Litinin din da ta gabata.
A ranar Talata ne dai rahotanni suka ce ‘yan ta’adda sun sake kai wani hari a tashar jirgin kasa ta Gidan da ke kan hanyar jirgin Abuja zuwa Kaduna.