fidelitybank

Harin jirgin ƙasa: Sajan Funtuwa ya rasu sakamakon raunukan da ya samu da ga harashi

Date:

 

 

Daya daga cikin wadanda harin jirgin ƙasan Abuja-Kaduna ya rutsa da su a ranar 28 ga Maris, Sajan Muhammad Haruna Funtua, ya rasu sakamakon raunuka da dama da ya samu ta harbin bindiga.

Rahotanni sun bayyana cewa an harbi mamacin ne a kai da kirji lokacin da ‘yan ta’addan suka far wa jirgin kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi da sauran fasinjojin.

Duk da cewa daga baya aka garzaya da shi mahaifarsa da ke Funtuwa, Jihar Katsina, domin jinya, amma ya rasu ne a ranar Talata, 5 ga Afrilu, 2022.

Wani ɗan uwan mamacin, mai suna Mallam Idris, ya tabbatar da rasuwar tsohon ma’aikacin.

A cewarsa, “Ya yi ta fama da raunukan amma da ga ƙarshe ya rasu. Muna rokon Allah ya jikansa da Aljannar Firdausi.”

Idan dai za a iya tunawa, kimanin fasinjoji takwas ne ‘yan ta’addan su ka kashe a cikin jirgin, yayin da wasu kuma suka samu raunuka daban-daban sakamakon harbin bindiga, sannan ‘yan ta’addan suka yi awon gaba da su zuwa wani wuri da ba a san inda suke ba.

 

hausa news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Sojojin hadin gwiwa sun hallaka ‘yan Boko Haram a tafkin Chadi

Rundunar hadin gwiwa mai yaƙi da Boko Haram a...

Na yi rashin aboki na gari kuma Najeriya ta rasa mutumin kirki – Tinubu

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, na ci gaba da alhinin...

Shettima ya jagoranci yi wa Buhari addu’o’i na musamman a Daura

An gudanar da addu'o'i na musamman don neman gafara...

Isra’ila ta kashe mana fararen hula – Syria

Shugaban Syria, Ahmed al-Sharaa ya zargi Isra'ila da kai...

Za mu koma fadar gwamnatin Katsina mu karbi gaisuwar Buhari – Radda

Gwamnan jihar Katsina, Dikko Umar Radda ya ce bayan...

Tinubu zai jagoranci yi wa Buhari addu’a

Shugaban Kasa, Bola Tinubu, zai jagoranci taron addu'o'i na...

Muƙarraban Buhari sun ci amanar da ya ba su lokacin mulkinsa – Bagos

Wani tsohon ɗan majalisar wakilai, Dachung Bagos ya bayyana...

Guardiola ya bude kofa ga ‘yan wasa shida su bar kungiyar

Kocin Manchester City, Pep Guardiola, a shirye yake ya...

Ba gudu ba ja da baya a zanga-zangar mu – Tsofaffin ‘Yansanda

Kungiyar ‘yan sandan Najeriya masu ritaya ta sanar da...

Malami ya magantu kan sukar rashawa a mulkin marigayi Buhari

Tsohon babban Lauyan Najeriya kuma ministan shari'a, Abubakar Malami,...

Turkiyya ta gargadi Najeriya kan ‘yan ta’addar FETO

Gwamnatin Turkiyya ta fitar da wani gargadin cewa, mambobin...

Kiristoci sun jinjinawa Musulmai yadda aka yi jana’izar Buhari ba kashe kudi

Ana samun karuwar al’ummar Kudancin Najeriya musamman mabiya addinin...
X whatsapp