Daya daga cikin wadanda harin jirgin ƙasan Abuja-Kaduna ya rutsa da su a ranar 28 ga Maris, Sajan Muhammad Haruna Funtua, ya rasu sakamakon raunuka da dama da ya samu ta harbin bindiga.
Rahotanni sun bayyana cewa an harbi mamacin ne a kai da kirji lokacin da ‘yan ta’addan suka far wa jirgin kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi da sauran fasinjojin.
Duk da cewa daga baya aka garzaya da shi mahaifarsa da ke Funtuwa, Jihar Katsina, domin jinya, amma ya rasu ne a ranar Talata, 5 ga Afrilu, 2022.
Wani ɗan uwan mamacin, mai suna Mallam Idris, ya tabbatar da rasuwar tsohon ma’aikacin.
A cewarsa, “Ya yi ta fama da raunukan amma da ga ƙarshe ya rasu. Muna rokon Allah ya jikansa da Aljannar Firdausi.”
Idan dai za a iya tunawa, kimanin fasinjoji takwas ne ‘yan ta’addan su ka kashe a cikin jirgin, yayin da wasu kuma suka samu raunuka daban-daban sakamakon harbin bindiga, sannan ‘yan ta’addan suka yi awon gaba da su zuwa wani wuri da ba a san inda suke ba.