Majalisar dattijai a ranar Talata ta koka kan harin da ‘yan ta’adda suka kai kan jirgin kasa da ke kan hanyar Kaduna ranar Litinin da kuma tabarbarewar yanayin tsaro a kasar baki daya.
Don haka ta yi kira ga sojoji da jami’an tsaro daban-daban da su kaddamar da cikakken yaki da ‘yan ta’adda da ‘yan bindiga a dukkanin kasar nan.
Ta kuma yi kira ga Sojoji da na sama da su rika kai hare-haren bama-bamai na maboyar ‘yan ta’addan.
Wadannan sun biyo bayan kudirin gaggawa ne wanda, Sanata Uba Sani (APC Kaduna ta tsakiya) ya dauki gabatar.
Sanata Sani wanda ya bi doka ta 41 da 51 na dokokin majalisar dattijai don a yi muhawara kan kudirin sa, ya koka da yadda harkokin tsaro a jihar Kaduna ke kara tabarbarewa a kullum tare da asarar rayuka da babu gaira babu dalili.