fidelitybank

Harin jirgin ƙasa: Sajan Funtuwa ya rasu sakamakon raunukan da ya samu da ga harashi

Date:

 

 

Daya daga cikin wadanda harin jirgin ƙasan Abuja-Kaduna ya rutsa da su a ranar 28 ga Maris, Sajan Muhammad Haruna Funtua, ya rasu sakamakon raunuka da dama da ya samu ta harbin bindiga.

Rahotanni sun bayyana cewa an harbi mamacin ne a kai da kirji lokacin da ‘yan ta’addan suka far wa jirgin kafin daga bisani jami’an tsaro su ceto shi da sauran fasinjojin.

Duk da cewa daga baya aka garzaya da shi mahaifarsa da ke Funtuwa, Jihar Katsina, domin jinya, amma ya rasu ne a ranar Talata, 5 ga Afrilu, 2022.

Wani ɗan uwan mamacin, mai suna Mallam Idris, ya tabbatar da rasuwar tsohon ma’aikacin.

A cewarsa, “Ya yi ta fama da raunukan amma da ga ƙarshe ya rasu. Muna rokon Allah ya jikansa da Aljannar Firdausi.”

Idan dai za a iya tunawa, kimanin fasinjoji takwas ne ‘yan ta’addan su ka kashe a cikin jirgin, yayin da wasu kuma suka samu raunuka daban-daban sakamakon harbin bindiga, sannan ‘yan ta’addan suka yi awon gaba da su zuwa wani wuri da ba a san inda suke ba.

 

legitnews

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Farfesa Jibril Aminu ya rasu ya na da shekaru 86

Allah ya yi wa Farfesa Jibril Aminu mai shekara...

Alhajin Najeriya ya rasu a tsayuwar Arfa

Wani Alhaji daga Najeriya ya rasu a filin Arfa...

Alhazai miliyan 1.673,230 ne ke gudanar da akin Hajji – GASTAT

Hukumar tattara alƙaluma ta Saudiyya (GASTAT) ta ce, Alhazai...

Isra’ila ta gano gawar ƴan ƙasarta

Rundunar sojin Isra'ila ta ce ta gano gawar ''yan...

Ma’aikatan wutar lantarki a Abuja sun fusata

Ma'aikatar kamfanin rarraba wutar lantarki na Abuja Electricity Distribution...

Ƴan Najeriya 147 da suka maƙale a Nijar sun dawo gida

Gwamnatin Najeriya ta tarɓi 'yan ƙasar 147 aka kwaso...

Alhazai Miliyan Ɗaya da Rabi ke tsayuwar Arfa

Dubun dubatar alhazai daga sassan duniya na hawan Arafa...

Sarkin Kano na 15 ya dakatar da yin hawan Sallah

Mai martaba Sarkin Kano na 15, Alhaji Aminu Ado...

Maniyacin jihar Kano da yake kokarin zama Alhaji ya rasu a Saudiyya

Daya daga cikin alhazan jihar Kano, Shu’aibu Jibrin, an...

Tinubu ya bayar da tallafin Biliyan Biyu da Tirela 20 na Shinkafa ga al’ummar Mokwa

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya ce, shugaban ƙasar...

Gwamna Adeleke na Osun ya gana da Tinubu

Gwamnan jihar Osun Ademola Adeleke ya kai ziyara ga...

An samu gawar mutane 7 a ambaliyar Neja

Rahotonni na cewa masu aikin ceto sun zaƙulo gawar...
X whatsapp