fidelitybank

Harin jirgin ƙasa: Muna cikin mawuyacin hali a kan ƴan uwan mu

Date:

‘Yan uwa da makusantan fasinjojin da ‘yan bindiga suka sace yayin harin da suka kai a jirgin kasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a makon jiya, sun bayyana mawuyacin halin da suke ciki tun bayan sace ‘yan uwan na su.

A ranar Litinin din makon jiya ne maharan da hukumomi suka ce ‘yan Boko Haram ne suka kai hari kan jirgin kasan lamarin da ya yi sanadin mutuwar fasinja takwas da jikkatar wasu da dama.

Makusanta da dangin fasinjojin na ci gaba da zaman zullumi, yayin da a karshen makon jiya hukumar kula da sufurin jiragen ƙasa ta kasa ta tabbatar cewa, fasinjoji fiye da 200 ne suka kuɓuta daga harin.

Wani dan uwan daya daga cikin fasinjojin wanda ba ya so a ambaci sunansa, ya shaida wa BBC Hausa cewa “Ubangiji ne kawai yake rike da mu, domin halin da muke ciki ba mai dadi ba ne, amma mun bar komai ga Allah.”

A sanarwa ta baya bayan nan da hukumar kula da sufurin jiragen ƙasa ta Najeriya ta fitar, ta ce, fasinja 362 ne a cikin jirgin da aka kai wa hari ranar 28 ga watan Maris din da ya gabata.

“An tabbatar da cewa fasinjoji 186 da suka shiga jirgin suna cikin koshin lafiya a gidajensu. Sannan akwai karin mutum 14 da su ma yau aka tabbatar sun tsira. Wayoyin salula na mutum 51 da suka shiga jirgin suna kashe ko kuma ba a iya samun su bayan kiran da aka yi musu tun daga ranar Talata da safe,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, fasinja 22 ne suka bata, kamar yadda ‘yan uwansu suka bayyana wa hukumar.

dailypost news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp