fidelitybank

Harin jirgin ƙasa: Muna cikin mawuyacin hali a kan ƴan uwan mu

Date:

‘Yan uwa da makusantan fasinjojin da ‘yan bindiga suka sace yayin harin da suka kai a jirgin kasan da ya tashi daga Abuja zuwa Kaduna a makon jiya, sun bayyana mawuyacin halin da suke ciki tun bayan sace ‘yan uwan na su.

A ranar Litinin din makon jiya ne maharan da hukumomi suka ce ‘yan Boko Haram ne suka kai hari kan jirgin kasan lamarin da ya yi sanadin mutuwar fasinja takwas da jikkatar wasu da dama.

Makusanta da dangin fasinjojin na ci gaba da zaman zullumi, yayin da a karshen makon jiya hukumar kula da sufurin jiragen ƙasa ta kasa ta tabbatar cewa, fasinjoji fiye da 200 ne suka kuɓuta daga harin.

Wani dan uwan daya daga cikin fasinjojin wanda ba ya so a ambaci sunansa, ya shaida wa BBC Hausa cewa “Ubangiji ne kawai yake rike da mu, domin halin da muke ciki ba mai dadi ba ne, amma mun bar komai ga Allah.”

A sanarwa ta baya bayan nan da hukumar kula da sufurin jiragen ƙasa ta Najeriya ta fitar, ta ce, fasinja 362 ne a cikin jirgin da aka kai wa hari ranar 28 ga watan Maris din da ya gabata.

“An tabbatar da cewa fasinjoji 186 da suka shiga jirgin suna cikin koshin lafiya a gidajensu. Sannan akwai karin mutum 14 da su ma yau aka tabbatar sun tsira. Wayoyin salula na mutum 51 da suka shiga jirgin suna kashe ko kuma ba a iya samun su bayan kiran da aka yi musu tun daga ranar Talata da safe,” in ji sanarwar.

Sanarwar ta kara da cewa, fasinja 22 ne suka bata, kamar yadda ‘yan uwansu suka bayyana wa hukumar.

nnn news today

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Majalisar dokoki na son Iran ta yanke hulɗa da hukumar sanya ido kan makamashin nukiliya

Majalisar dokokin Iran ta kaɗa ƙuri’a domin yanke hulɗa...

Ƴan sanda sun kama mutum 26 da ake zargi da hannu a kashe-kashen Benue

Sufeto Janar na ‘ƴan sanda, Kayode Egbetokun, ya bayyana...

Ba dan mun yi wa Iran barna ba da har yanzu ba ta nemi sulhu ba – Trump

Shugaban Amurka, Donald Trump, ya sake jaddada cewa harin...

Iran ta zartar da hukuncin kisa kan masu leken asiri

Kamfanin dillancin labarai na sashen shari'a a Iran ya...

Za mu ɗauki matakin hana sake faruwar kisan mutane – Gwamnatin Filato

Gwamnatin jihar Filato ta jaddada aniyarta ta ɗaukar mataki...

Babu barazanar tsaro a Abuja – Najeriya

Gwamnatin Tarayya ta ce, babu wata barazanar a babban...

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...
X whatsapp