A cigaba da luguden wuta da Isra’ila ke yi a ƙasar Lebanon, wani rahoto da kamfanin dillancin labarai na Reuters ya fitar, ya nuna cewa wani hari da Isra’ila ta kai a cikin dare ya kashe mutum tara ƴan gida ɗaya, ciki har da ƙananan yara huɗu.
Reuters ta ruwaito Magajin Gari Mohammad Saaba yana tabbatar da lamarin, inda ya ce harin ya auku ne a garin Shebaa na kudancin Lebanon. In ji BBC.
A ɗaya gefen kuma, Hezbollah ta ce ta kai hare-hare guda biyu a yankunan Tiberias da Kiryat Ata.