Kafofin yaɗa labaran Siriya sun ce, Isra’ila ta ƙaddamar da hare-hare kan manyan filayen jiragen samanta biyu.
Kamfanin dillancin labaran ƙasar ya ce an kai wa filayen jiragen saman Damascus da na Aleppo hare-hare.
Aƙalla fararen hula biyu da ke aiki a filin jirgin saman Damascu aka kashe, kamar yadda kamfanin dillancin labarai na Reuters ya ambato hukumomin ƙasar na bayyanawa.
Ba jigilar fasinjojin kaɗai filayen jiragen Damascus da na Aleppo ke yi ba, har da zamansu sansanin sojin ƙasar.
Inda wasu rahotonni ke zargin filayen jiragen biyu da zama cibiyar jigilar makaman da Iran ke aike wa Hezbollah, ƙungiyar mayaƙan da ke da ƙarfi a ƙasashen Siriya da Lebanon.