Gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, ya ce, harin da aka kai ranar Litinin a babban ofishin INEC da ke Owerri ya nuna cewa akwai hannun ‘yan siyasa a matsalar tsaron da ke addabar jihar.
Da yake jawabi ga manema labarai a shalkwatar ‘yan sanda a yau, gwamnan ya ce masu tsatsauran ra’ayi ne suka kai harin.
“A wannan jihar akwai ‘yan siyasar da ke son lashe zabe kota halin kaka ba tare da bin tsari ba,” in ji Uzodinma.
Gwamnan ya kara da cewa ” Ina jin dadin aikin ‘yan sanda da sauran jami’an tsaro. Kuma zamu ci gaba da basu goyon baya.”
Uzodinma ya yi alkawarin cewa lamuran tsaro za su inganta kafin bukukuwan kirismeti.