fidelitybank

Harin da a ka kai shalkwatar ‘yan sandan Adamawa ya jefa mutane firgici

Date:

An kai hari hedikwatar ‘yan sanda da ke Adamawa a sanyin safiyar Laraba, lamarin da ya ɗaga hankula da jefa al’umma cikin yanayi na kaɗuwa a birnin Yola.

An shafe kusan rabin sa’a ana harbe-harbe, a cewar mazauna kusa da hedikwatar.

Wasu majiyoyi na cewa sojoji ne suka kai harin na ramuwa, bayan sun zargi wani ɗan sanda da kashe wani jami’insu.

Wata sanarwa da kwamishinan ‘yan sanda CP Afolabi Babatola, ya fitar ta tabbatar da harin tare da Allah-wadai da rikicin da ya ɓarke tsakanin jami’an ‘yan sanda da sojoji.

A cewar sanarwar rikici ne ya rikiɗe zuwa musayar harbe-harben bindiga wanda ya kai ga wani mummunan hari kan ofishin ‘yan sanda da ya yi sanadin mutuwar wani Sufeto, Jacob Daniel.

CP Babatola ya bayar da umarnin a gudanar da bincike cikin gaggawa domin tabbatar da adalci da kuma dawo da zaman lafiya.

Ya kuma jaddada cewa ba za a sake lamuntar duk wani hari da ake kai wa jami’an tsaro a bakin aiki.

Babatola ya jaddada muhimmanci rayuwar dukkanin jami’an tsaro tare da shan alwashin cewa za a magance irin waɗannan rikice-rikicen bisa dokokin da ake dasu.

Kwamishinan ya kuma bayyana kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da yin kira da a haɗa kai a tsakanin rundunonin tsaro domin kare haƙƙinsu.

CP Babatola ya kuma buƙaci jama’a su kwantar da hankulansu, inda ya tabbatar cewa manyan jami’an tsaron biyu na aiki tukuru bisa tsarin doka don shawo kan duk wata matsala ta tsaro.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Iran ta dakatar da tashin jirgi a ƙasarta

Hukumar kula da zirga-zirgar jiragen sama ta Iran ta...

Poland za ta kwashe dukkannin ƴan ƙasarta daga Isra’ila

Poland na shirin kwashe kusan ‘yan kasarta 200 daga...

Kisan Binuwai abun haushi ne bai kamata a ƙyale ba – Atiku

Atiku Abubakar ya yi Allah-wadai da Kisan Benue, tare...

Ƴan Bindiga sun ajiye makamai a Katsina

Wasu fitattun jagororin ƴanbindiga da suka addabi yankunan ƙaramar...

Iran ta rataye Mutumin da ya yi mata leƙen asiri

Iran ta ce ta aiwatar da hukuncin kisa ga...

Isra’ila ta ci gaba da neman Mutanen da suka maƙale

Tawagar masu aikin ceto a Isra'ila na ci gaba...

Kotu ta bayar da umarni a kashe Matashi ɗan shekara 23 a Kano

Babbar kotun jihar Kano mai lamba 23 ƙarƙashin mai...

Iran ta na ci gaba da luguden makami a kan Isra’ila

Iran ta ci gaba da lugudan wuta a Isra'ila...

An yi sulhu da shugabannin ƴan Bindiga a Katsina

Wasu al'ummar Katsina, sun yi sulhu da wasu shugabannin...

Za a fuskanci ambaliya a wasu jihohin – NIMET

Hukumar kula da yanayi ta NiMet, ta ce akwai...

Za mu mayar wa da Isra’ila martani mai tsanani – Iran

Shugaban ƙasar Iran, Masoud Pezeshkian, ya yi alwashin mayar...

Ba za mu taɓa barin Iran ta ƙera makamai masu linzami ba – Isra’ila

Firaministan Isra'ila, Benjamin Netanyahu, ya ce burin ƙasarsa shi...
X whatsapp