fidelitybank

Harin da a ka kai shalkwatar ‘yan sandan Adamawa ya jefa mutane firgici

Date:

An kai hari hedikwatar ‘yan sanda da ke Adamawa a sanyin safiyar Laraba, lamarin da ya ɗaga hankula da jefa al’umma cikin yanayi na kaɗuwa a birnin Yola.

An shafe kusan rabin sa’a ana harbe-harbe, a cewar mazauna kusa da hedikwatar.

Wasu majiyoyi na cewa sojoji ne suka kai harin na ramuwa, bayan sun zargi wani ɗan sanda da kashe wani jami’insu.

Wata sanarwa da kwamishinan ‘yan sanda CP Afolabi Babatola, ya fitar ta tabbatar da harin tare da Allah-wadai da rikicin da ya ɓarke tsakanin jami’an ‘yan sanda da sojoji.

A cewar sanarwar rikici ne ya rikiɗe zuwa musayar harbe-harben bindiga wanda ya kai ga wani mummunan hari kan ofishin ‘yan sanda da ya yi sanadin mutuwar wani Sufeto, Jacob Daniel.

CP Babatola ya bayar da umarnin a gudanar da bincike cikin gaggawa domin tabbatar da adalci da kuma dawo da zaman lafiya.

Ya kuma jaddada cewa ba za a sake lamuntar duk wani hari da ake kai wa jami’an tsaro a bakin aiki.

Babatola ya jaddada muhimmanci rayuwar dukkanin jami’an tsaro tare da shan alwashin cewa za a magance irin waɗannan rikice-rikicen bisa dokokin da ake dasu.

Kwamishinan ya kuma bayyana kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da yin kira da a haɗa kai a tsakanin rundunonin tsaro domin kare haƙƙinsu.

CP Babatola ya kuma buƙaci jama’a su kwantar da hankulansu, inda ya tabbatar cewa manyan jami’an tsaron biyu na aiki tukuru bisa tsarin doka don shawo kan duk wata matsala ta tsaro.

besda salary

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp