An kai hari hedikwatar ‘yan sanda da ke Adamawa a sanyin safiyar Laraba, lamarin da ya ɗaga hankula da jefa al’umma cikin yanayi na kaɗuwa a birnin Yola.
An shafe kusan rabin sa’a ana harbe-harbe, a cewar mazauna kusa da hedikwatar.
Wasu majiyoyi na cewa sojoji ne suka kai harin na ramuwa, bayan sun zargi wani ɗan sanda da kashe wani jami’insu.
Wata sanarwa da kwamishinan ‘yan sanda CP Afolabi Babatola, ya fitar ta tabbatar da harin tare da Allah-wadai da rikicin da ya ɓarke tsakanin jami’an ‘yan sanda da sojoji.
A cewar sanarwar rikici ne ya rikiɗe zuwa musayar harbe-harben bindiga wanda ya kai ga wani mummunan hari kan ofishin ‘yan sanda da ya yi sanadin mutuwar wani Sufeto, Jacob Daniel.
CP Babatola ya bayar da umarnin a gudanar da bincike cikin gaggawa domin tabbatar da adalci da kuma dawo da zaman lafiya.
Ya kuma jaddada cewa ba za a sake lamuntar duk wani hari da ake kai wa jami’an tsaro a bakin aiki.
Babatola ya jaddada muhimmanci rayuwar dukkanin jami’an tsaro tare da shan alwashin cewa za a magance irin waɗannan rikice-rikicen bisa dokokin da ake dasu.
Kwamishinan ya kuma bayyana kudirin rundunar na kare rayuka da dukiyoyin jama’a tare da yin kira da a haɗa kai a tsakanin rundunonin tsaro domin kare haƙƙinsu.
CP Babatola ya kuma buƙaci jama’a su kwantar da hankulansu, inda ya tabbatar cewa manyan jami’an tsaron biyu na aiki tukuru bisa tsarin doka don shawo kan duk wata matsala ta tsaro.