fidelitybank

Hareran Ta’addanci: Majalisa ta gayyaci shugabannin tsaro

Date:

Shugabannin tsaro a Najeriya za su bayyana a gaban Majalisar Wakilai, bayan majalisa ta umarce su da yin hakan a zamanta na jiya Laraba.

Sai dai tun a Larabar shugabannin tsaron suka nemi su gana da shugabancin majalisar ƙarƙashin Mataimakin Kakakin Majalisa Ahmed Idris Wase, amma sai majalisar ta ƙi yarda da hakan, tana mai tilasta musu bayyana a gabanta a yau Alhamis.

Majalisar dai na son hafsohin tsaron su yi mata ƙarin bayani ne g ame da yadda ‘yan fashi suka kai hari kan jirgin ƙasa na Kaduna zuwa Abuja ranar Litinin, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar aƙalla mutum takwas.

Kazalika, tana so ta ji yadda ‘yan bindigar suka kai wani harin kan filin jirgin sama na Kaduna kwana biyu kafin na jirgin ƙasan.

Waɗanda majalisar ke son su bayyana a gabanta sun haɗa da hafsoshin tsaron ƙasa, da sufeton ‘yan sanda na ƙasa, da ministocin da lamarin ya shafi ma’aikatunsu bisa umarnin shugabannin kwamatocin soja da na sufurin jirgin sama da na ‘yan sanda da na sufuri.

Da ƙarfe 3:00 agogon ake sa ran za su bayyana a zauren majalisar.

nigerianews.com

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Isra’ila za ta mayarwa da Iran martani duk da tsagaita wuta

Ministan tsaron Isra'ila, Katz ya bayyana cewa, ya ba...

Ba mu kai wa Isra’ila hari ba – Iran

Kafar watsa labarai ta Iran ta ruwaito gwamnatin ƙasar...

Duk da faduwar farashin mai NNPCL ya kara farashi

Kamfanin man fetur na Najeriya, NNPCL ya ƙara farashin...

Duk wasu ƙawayen Amurka za su ɗanɗanar kuɗarsu – Iran

Rundunar dakarun juyin juya halin Iran ta fitar da...

Iran ta mayar da martani kan sojojin Amurka dake Qatar

Kafofin yaɗa labaran Iran sun bayyana cewa ƙasar ta...

Faransa ba ta goyon bayan Amurka na kifer da gwamnatin Iran – Barrot

Ministan harkokin wajen Faransa ya ce, ƙasarsu ba ta...

Kotu a Kano ta ɗaure masu satar Yara

Babbar kotun jihar Kano da ke zamanta a Miller...

Ba wata hujja da Amurka za ta kai wa Iran hari – Rasha

An gudanar da tattaunawa tsakanin shugaban Rasha Vladimir Putin...

Tinubu ya miƙa saƙon ta’aziyya ga mutanen Kano da Kaduna da Borno

Shugaba Bola Tinubu ya yi Alla-wadai da kisan wasu...

Amurka ta tafka babban kuskure – Iran

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya yi Alla-wadai...

Trump ya yaudari Amurkawa da Iran – Aragachi

Ministan harkokin wajen Iran, Abbas Araghchi ya bayyana cewa...

Sai an hukunta Mutanen da suka kashe ƴan ɗaurin aure – Uba Sani

Gwamnan jihar Kaduna Uba Sani ya yi Alla-wadai da...
X whatsapp