fidelitybank

Harda Sojojin sama su biyar daga cikin mutane 19 da suka rasu a haɗarin Filato

Date:

Wasu sojojin sama na Najeriya biyar na daga cikin matafiya 19 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a Hawan Kibo da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato a jiya Talata.

A wata sanarwa da kakakin rundunar sojin sama ta Najeriya, Olusola Akinboyewa ya fitar, ya ce, sojojin na kan hanyarsu ne ta zuwa wani wasa a Abuja, lokacin da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota.

Sai dai kuma wani bayani da hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya ta fitar ya saɓa da wanda kakakin sojin ya fitar, inda hukumar ta ce motar bas ta sojojin ƙirar Hiace, mai ɗaukar mutum 18 da ta taso daga Yola ta bi yo ta Jos a kan hanyarta ta zuwa Abuja ta ci karo ne da tirela wadda ke tsaye a kan hanya, lamarin da ya janyo mutuwar direban da dukkanin sauran mutanen da ke cikin motar su 18.

A wata hira da tasahar talabijin ta Channels, kakakin hukumar ta kiyaye haɗura (FRSC) a jihar ta Filato, Peter Longsan, ya ce dukkanin mutanen da ke cikin wannan mota bas da sojojin suke sun mutu.

Longsan ya danganta munin haɗarin da ya kai ga mutuwar mutanen gaba ɗaya, da gudun da direab bas ke yi inda ya ce a dalilin hakan ne da ta yi karo da tirelar ba wanda ya tsira.

daily 
post news paper

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp