Oluwo na Iwoland, Oba Abdulrosheed Adewale Akanbi, a ranar Lahadin da ta gabata, ya bayyana rashin jin dadinsa game da rarrabuwar kawuna tsakanin shugabannin siyasar Yarbawa, gabanin babban zabe na 2023.
Ya ce ya yi mamakin irin yadda ake samun rarrabuwar kawuna a tsakanin shugabannin siyasar Yarbawa a jam’iyyun APC da PDP, yana mai cewa hakan na nuni da rashin hadin kai.
Ya kira jagoran jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa, Asiwaju Bola Ahmed Tinubu, Cif Bisi Akande, mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo, da dukkan gwamnonin Kudu maso Yamma, yana mai cewa ba za a yafe musu ba idan har suka kasa haska arzikin kasar Yarbawa kafin 2023 babban zaben 2023.
Oluwo a cikin wata sanarwa da sakataren yada labaran sa, Alli Ibrahim, ya fitar, ya bukaci Tinubu ya sake hada gidansa na siyasa domin amfanin kabilar Yarbawa. In ji Daily Trust.