fidelitybank

Haramcin ciran kudade ba zai cutar da gwamnoni ba – NFIU

Date:

Hukumar tattara bayanan sirri kan sha’anin kuɗi ta kasa ”Nigerian Financial Intelligence Unit” (NFIU), ta ce haramcin da take ƙoƙarin sanyawa kan cire kuɗi daga asusun gwamnatin tarayya da na jihohi abu ne ba zai taimaka wa gwamnonin ba cutar da su ba.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Ahmed Dikko sa’o’i bayan ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta soki sanarwa da hukumar ta fitar ranar 5 ga watan Janairu, ta umartar bankuna da su dakatar da bai wa gwamnoni kudaɗe daga asusun gwamnati daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

“Sabuwar dokar da hukumar NFIU ke shirin ƙaƙabawa game da sha’anin shige da ficen kuɗi baya cikin tsarin dokokin da ayyukan hukumar” Kamar yadda ƙungiyar gwamnonin ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Ƙungiyar gwamnonin ta kuma kafa kwamiti mai mambobi shida da za su tattauna da babban bankin ƙasar domin duba batun matsalolin sha’anin harkokin kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

A martanin da hukumar ta NFIU ta fitar ta ce a shirye take domin hada kai da kwamitin da ƙungiyar gwamnonin ta kafa domin wayar musu da kai game muhimmancin sabon kuɗurin.

”Sannan abun da muke ƙoƙarin aiwatarwa bai saɓa doka ba. Mun bayar da ƙa’idar ne domin magance tarin bincike da muka hango wa gwamnonin. Mun sanya ƙa’idar ce domin taimaka wa gwamnonin ba don cutar da su ko wani ma’aikacin gwamnati ba” kamar yadda sanarwar da NFIU ta fitar.

Sannan kuma hukumar ta ce a baya ta sanya makamanciyar wannan doka kan ƙananan hukumomi, inda aka kai ta kotu, amma kuma sai ta yi nasara a kotun.

thisday nigeria news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

An gargadi al’umma su yi taka tsan-tsan da ambaliyar ruwan sama

Yayin da ake ci gaba da fuskantar saukar ruwan...

Gwamnatin Tarayya za ta gina hanyar sufurin jirgin ƙasa a Kano

Gwamnatin Tarayya ta ce, za ta samar da titin...

Abin da ya sa muke ci gaba da tsare Sowore – Ƴansanda

Kwamishinan ƴansanda mai kula da sashen kai ɗauki na...

INEC za ta bai wa ɗaurarru damar kaɗa ƙuri’a a lokacin zaɓuka

Hukumar zaɓen Najeriya, INEC ta ta duba yiwuwar bai...

Mai ya jawo Matan Zamfara su ka yi zanga-zanga

Ɗaruruwan mata ne tsofaffi da masu shawarya suka gudanar...

Aƙalla mutane 24,000 ne suka ɓata saboda Boko Haram a Najeriya

Kungiyar Agaji ta Red Cross ta bayyana cewa aƙalla...

‘Yansanda ku gaggauta sakin Sowore – Obi

Tsohon ɗan takarar shugaban kasa a jam'iyyar LP, Peter...

PDP ta gargaɗi mambobinta kan goyon bayan Tinubu

Babbar jam'iyyar hamayya ta PDP a Najeriya ta gargaɗi...

Mashawarcin gwamnan Kano ya rasu bayan harin ‘yan Daba

Sadiq Gentle, babban mai ba da rahoto na musamman...

An fitar da jerin sunayen Matasan ‘yan wasan da za su lashe kyautar Kopa

Masu shirya kyautar Ballon d’Or, sun fitar da jerin...

An fitar da jerin masu tsaron raga da za su lashe kyautar gwarzon bana

An fitar da sunayen wadanda za a zaba don...

Jonathan ne ya fi cancanci ya rike Najeriya Farfesa Tukur

Farfesa Tukur Muhammad-Baba, Sakataren Yada Labarai na Kungiyar Tuntuba...
X whatsapp