fidelitybank

Haramcin ciran kudade ba zai cutar da gwamnoni ba – NFIU

Date:

Hukumar tattara bayanan sirri kan sha’anin kuɗi ta kasa ”Nigerian Financial Intelligence Unit” (NFIU), ta ce haramcin da take ƙoƙarin sanyawa kan cire kuɗi daga asusun gwamnatin tarayya da na jihohi abu ne ba zai taimaka wa gwamnonin ba cutar da su ba.

Hukumar ta bayyana hakan ne a wata sanarwa da ta fitar ranar Asabar ta hannun jami’inta na hulda da jama’a Ahmed Dikko sa’o’i bayan ƙungiyar gwamnonin ƙasar ta soki sanarwa da hukumar ta fitar ranar 5 ga watan Janairu, ta umartar bankuna da su dakatar da bai wa gwamnoni kudaɗe daga asusun gwamnati daga ranar 1 ga watan Maris mai zuwa.

“Sabuwar dokar da hukumar NFIU ke shirin ƙaƙabawa game da sha’anin shige da ficen kuɗi baya cikin tsarin dokokin da ayyukan hukumar” Kamar yadda ƙungiyar gwamnonin ta bayyana a wata sanarwa da ta fitar.

Ƙungiyar gwamnonin ta kuma kafa kwamiti mai mambobi shida da za su tattauna da babban bankin ƙasar domin duba batun matsalolin sha’anin harkokin kuɗi da ƙasar ke fuskanta.

A martanin da hukumar ta NFIU ta fitar ta ce a shirye take domin hada kai da kwamitin da ƙungiyar gwamnonin ta kafa domin wayar musu da kai game muhimmancin sabon kuɗurin.

”Sannan abun da muke ƙoƙarin aiwatarwa bai saɓa doka ba. Mun bayar da ƙa’idar ne domin magance tarin bincike da muka hango wa gwamnonin. Mun sanya ƙa’idar ce domin taimaka wa gwamnonin ba don cutar da su ko wani ma’aikacin gwamnati ba” kamar yadda sanarwar da NFIU ta fitar.

Sannan kuma hukumar ta ce a baya ta sanya makamanciyar wannan doka kan ƙananan hukumomi, inda aka kai ta kotu, amma kuma sai ta yi nasara a kotun.

the sun news

Subscribe to Our VIP Newsletter

[newsletter_signup_form id=1]

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Share post:

Popular

More like this
Related

Gwamnatin Tinubu ta kama-karya ce – Atiku

Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar ya ce, hare-haren...

An gayyaci El-Rufa’i ka n zargin tayar da rikici a Kaduna

Rundunar ƴansandan jihar Kaduna, sun buƙaci tsohon gwamnan jihar...

Badakalar Naira biliyan 1.17 ta sake kunno kai a gwamnatin Kano

Rikicin rashawa da ya dabaibaye gwamnatin jihar Kano ya...

Ba za mu daga kafa ga duk wanda ya takale mu ba – China

Shugaba Xi Jinping na China, ya ce babu wani...

Nigeria Air ba na bogi ba ne – Hadi Sirika

Tsohon Ministan sufurin jiragen sama na Najeriya, Hadi Sirika,...

Amurka ta mika wa Najeriya tallafin abinci miliyan 32.5

Gwamnatin Amurka ta bayar da tallafin dala miliyan 32.5...

Gwamnatin Kano ta gargadi kungiyar ACF

Gwamnatin jihar Kano ta gargaɗi ƙungiyar Arewa Consultative Forum...

Operation Kukan Kura ya yi aiki sosai a Kano – CP Bakori

Hukumar ‘Yan Sanda ta Jihar Kano ta kaddamar da...

An sanya dokar ta bace a Makabartun Kano

Shugaban ƙaramar hukumar Nassarawa a Kano Honarabul. Yusuf Shuaibu...

An ga ‘Yar shekara 13 Fatima a rataye a Kano

Iyaye da sauran ‘yan uwa na cikin juyayi kan...

‘Yansanda sun kama Linga da Guchi rikakkun ‘yan Daba a Kano

Rundunar ’yan sandan jihar Kano ta kama Mohammed Isma’il...

Tinubu ya sauka da kwari bayan ya dawo daga Brazil

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya koma Najeriya bayan kammala...
X whatsapp