Babban Daraktan kungiyar Patriot for Advancement of Peace and Social Development Dr Sani Abdullahi Shinkafi ya caccaki gwamnonin Arewa da suka bijirewa kudirin gyara haraji.
A wata hira da ya yi da tashar talabijin ta Arise TV a ranar Litinin, Shinkafi ya bayyana gwamnonin a matsayin “lalalai” kuma ba sa son bullo da dabarun samar da kudaden shiga na cikin gida.
A cewarsa, gwamnonin da ke ikirarin cewa kudaden harajin zai kara wahalhalu a yankin arewacin kasar “su ne suka haddasa tabarbarewar tattalin arziki, da rashin tsaro, da rashin aikin yi, da talauci, da koma bayan ilimi a yankin Arewa.
Shinkafi ya kare kakkausar murya kan kudirin sake fasalin harajin da ake ta cece-kuce da su, musamman daga gwamnonin arewa, yana mai bayyana ‘yan adawa a matsayin siyasa ce da kuma rashin fahimtar juna.
Shinkafi ya kuma ce “Harin da Majalisar Matasan Arewa ta kai ba shi ne ya kamata a yi ba,” yana mai jaddada cewa Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa, wanda ya jagoranci zaman, yana aiwatar da ayyukansa na tsarin mulki.